Adabi

Haiku wata waƙa ce da ta samo asali ko tushe daga ƙasar Japan – Tijjani M. Musa 

Haiku wata waƙa ce da ta samo asali ko tushe daga ƙasar Japan – Tijjani M. Musa 

"Marubuta na ba da gudunmawa muhimmiya kuma mafi tsoka a fagen shirya fim" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  A makon jiya mun kawo muku kashin farko na tattaunawar da muka yi da tsohon Shugaban ƙungiyar Marubuta ta ANA reshen Kano, masanin harkar jarida, da zayyanar taswirar gidaje da muhalli, Tijjani Muhammad Musa. Don haka yanzu sai ku gyara zama ku cigaba da jin wannan tattaunawa da suka yi da Abba Abubakar Yakubu, wacce ke cike da fasaha da ilimi, irin na gogaggun manazarta adabi. MANHAJA: Gaya mana abin da ya ja hankalinka ga salon rubutun waƙe irin na Haiku? ARC. TIJJANI:…
Read More
Nasarorin da na samu a harkar rubutu ba irin waɗanda sauran marubuta ke lissafawa ba ne – Tijjani Muhammad Musa

Nasarorin da na samu a harkar rubutu ba irin waɗanda sauran marubuta ke lissafawa ba ne – Tijjani Muhammad Musa

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU MANHAJA: Mu fara da jin cikakken sunanka? ARC. TLIJANI: Cikakken sunana shi ne Arc. Tijjani Muhammad Tajuddin Musa. Ina yi wa kaina laƙabi da Muhammad Tajajjini. Wasu kuma da suka sanni tun muna yara ƙanana su kan kira ni da Tajo kai tsaye. Ni marubucin adabi ne kuma ina rubuce-rubucena cikin harsuna biyu wato Hausa da Turanci. Ina rubuta rubutattun waƙoƙi na Turanci da na Hausa da kuma rubutun zube. Har ila yau ni gogaggen ɗan Jarida ne, kuma cikakken mamba na Ƙungiyar Ƙwararrun 'Yan Jarida a fannin rediyo da talabijin wato SNB. Sannan na samo…
Read More
Wasu marubutan da suka samu ɗaukaka suna da girman kai –  Fatima Sunusi Rabi’u 

Wasu marubutan da suka samu ɗaukaka suna da girman kai –  Fatima Sunusi Rabi’u 

"Sanadin kyautar da aka min a dalilin rubutu na samu jarin sana'ata" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Fatima Sunusi Rabi'u, ba marubuciyar onlayin ba ce kawai, tana daga cikin marubutan da suka wallafa littattafansu a tsarin ɗab'i, har ma suka shiga kasuwa. Bayan kasancewarta ƴar kasuwa, tana matuƙar sha'awar aikin jarida na gidan rediyo. Ta rubuta littattafai da gajerun labarai fiye da goma, kuma har yanzu tana kan cigaba da rubutu. A ganawarta da wakilinmu Abba Abubakar Yakubu, marubuciyar da ake yi wa laƙabi da Ummu Affan ta bayyana masa burinta na ganin an samu canji a harkar rubutun adabi da…
Read More
Dangantakar adabi da al’adu

Dangantakar adabi da al’adu

Adabi shi ne ruwan da ke shayar da al'adu - Malam Abubakar Liman Daga AISHA ASAS Idan ana magananar adabi mutane na kallonsa a matsayin wata duniya daban da ba ta da alaƙa da al'adun alƙaryar da ke yin sa, wanda ya sa wasu ganin ba ta inda biyun suke da alaƙa. A 'yan kwanankin nan na ji wasu suna gardama kan littafan Hausa, wadda wata ta ke masu kallon ababen da ke ɓata tarbiyya tare da gurɓata al'adun Hausa. Ta yi amfani da kalmar "adabin nan ba abinda yake face ɓata al'adunmu." Wannan ne ya sa ni tambayar anya…
Read More
Kare martabar mata da yaƙi da fyaɗe ya sa na fara rubutu – Jidda Washa

Kare martabar mata da yaƙi da fyaɗe ya sa na fara rubutu – Jidda Washa

"Shirya gasar marubuta babban cigaba ne ga marubuci" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Daya daga cikin matasan marubuta da tauraruwar su ke haske cikin jerin marubuta mata da ke sakin rubuce-rubucen su a kafafen sada zumunta na 'online', Malama Jidda Washa, wacce ta rubuta littattafai da gajerun labarai da dama da ke ɗauke da darussa daban daban na kyautata rayuwa.  A tattaunawar ta da Blueprint Manhaja, marubuciyar ta bayyana abin da ya fara zaburar da ita ta fara rubutu, da burin ta a harkar adabi. MANHAJA: Ko za ki gabatar mana da kanki? JIDDA: Sunana Hauwa'u Adam Suleiman wacce aka fi…
Read More
Aikin jarida da rubutun adabi na tafiya kafaɗa da kafaɗa – Hajaru Baba Sakkwato

Aikin jarida da rubutun adabi na tafiya kafaɗa da kafaɗa – Hajaru Baba Sakkwato

"Gudunmawar marubuta wajen gyaran al'umma ba kaɗan ba ce" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Malama Hajaru Abdullahi Baba fitacciyar 'yar jarida ce da ke aiki a tashar rediyo ta ɓision FM a garin Sakkwato Birnin Shaihu. Marubuciya ce da ta samu nasarar wallafa littafin ta na farko mai suna 'Kishiyar mafalki' kimanin shekaru goma da suka gabata, amma halayyar wasu 'yan kasuwar littattafan Hausa marasa tausayi ya sa ta tsorata da harkar buga littafi, ta koma tunanin sakin rubuce-rubucen ta na gaba a yanar gizo wato 'online' kawai. A tattaunawar ta da Blueprint Manhaja, marubuciyar wacce kuma har wa yau 'yar…
Read More
Gudunmawar marubuta ga cigaban ƙasa

Gudunmawar marubuta ga cigaban ƙasa

Daga JIBRIN YUSUF KAILA A yayin da ýan Nijeriya ke cigaba da bayyana farincikinsu da murna albarkacin cika shekaru 65 da samun ýancin kan Nijeriya daga turawan mulkin mallaka na ƙasar Ingila, lallai ya kamata mu tambayi kawunanmu, wacce gudunmawa ce marubuta ya kamata su taka don samar da cigaban ƙasa?  Tabbas muna cikin wani lokaci da Nijeriya ke cikin buki da murna, ya zama wajibi ga kowanne ɗan ƙasa nagari, ya yi nazari da kyau don tunawa da gwagwarmayar da mazan jiya suka yi wajen samar wa ƙasar nan 'yancin kai. Dole mu kasance masu duba abin da ya…
Read More
Sharhin littafin ‘Asalin Labarina’

Sharhin littafin ‘Asalin Labarina’

Daga BAMAI A. DABUWA KKM Sunan Littafi: Asalin Labarina. Marubuci: Ayuba Muhd Danzaki. Shekarar Bugu: 2022. Bugu: AGP Computers Fagge. ISBN: Babu. Shafi: 144. Yanayi: Damina. Jigo: Soyayya da Zamantakewa. Salo: Fagen Waje. Mai Sharhi: Bamai A. Dabuwa Kkm. Gabatarwa/Tsokaci: 'Asalin Labarina', labari ne na wani matashin mai kuɗi Ziya'u wanda ya haɗu da matsalolin rayuwa kala-kala. Matsalolin da idan aka jarrabi jahili da su sai ya ɗaga kai sama da cewa wai me na maka ne? Duk da haka shi ya yi haƙuri, kodayake, ya mutum zai yi da abin da ya fi ƙarfin wuta wai inji kishiyar ƙonanniya.…
Read More
Ina rubutu ne don yaɗa koyarwar addini da kyawawan al’adun Arewa – Fatima Bala 

Ina rubutu ne don yaɗa koyarwar addini da kyawawan al’adun Arewa – Fatima Bala 

"Na yi mamakin yadda littattafaina suka samu karɓuwa a sassan Nijeriya da Afirka" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Fatima Bala, wata marubuciya ce ýar Nijeriya da tauraronta ke haskawa, ba a Arewa kaɗai ba, har ma da wasu sassan Afirka. Kodayake rubutun da take yi da harshen Turanci ya fi mayar da hankali ne kan rayuwar ýan Arewa a Turai, musamman a ƙasar Kanada inda take zaune tare da iyalinta, amma muhimman darussan da take fitowa da su da suka shafi hukunce-hukuncen addini da tarbiyya, ya sa ta yi fice a tsakanin marubuta da manazarta a Nijeriya. Wakilin Blueprint Manhaja, Abba…
Read More
Rasuwar Marubuciya Hauwa Ƙamshi ta girgiza duniyar marubuta Hausa

Rasuwar Marubuciya Hauwa Ƙamshi ta girgiza duniyar marubuta Hausa

Daga AISHA ASAS A jiya ne aka wayi gari duniyar marubuta Hausa ta girgiza sakamakon rasuwar ɗaya daga cikin fitattun marubuta mata, Hauwa Abubakar Lawal Maiturare, wacce ake kira da ƙamshi bayan gajeriyar rashin lafiya.  Hauwa ƙamshi ta rasu ne bayan ‘yan uwa da abokan arziki sun yi mata rakita zuwa sabon gidan da ta gina kuma ta tare a ranar Laraba, inda majiyar Blueprint Manhaja ta shaida mana cewa, a maraicen ranar ne ta yi ƙorafin kanta da jikinta na ciwo, don haka ta buƙaci ta kwanta ta ɗan huta. Bayan kwanciyar dai sai jikin ya rikice. Nan da…
Read More