26
Mar
Daga UMAR M. GOMBE Wata babbar kotu a jihar Akwa-Ibom ta yanke wa Farfesa Peter Ogban hukuncin zaman kaso na shekara uku bayan da ta kama shi da laifin tafka maguɗin zaɓe. Kotu ta kama malamin da laifin shirya sakamakon zaɓe na ƙarya tare da sanar da sakamakon yayin babban zaɓen 2019 a matsayinsa na shugaban zaɓe a shiyyar Akwa-Ibom ta Arewa maso-yamma. Farfesan wanda malami ne a Jami'ar Calabar a Sashen Nazarin Harkokin Noma, ya tafka maguɗi wajen haɗa sakamon wasu ƙananan hukumomi guda biyu a wancan lokaci, wato ƙaramar hukumar Oruk Anam da Etim Ekpo. A can baya,…
