18
Apr
Daga AISHA ASAS Babbar jam'iyyar bamayya a Nijeriya, PDP, ta ce duk da dai tana yi wa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari barka da dawowa daga jinyar da ya je a Turai, amma ba ta yi na'am da zancen shugaban ba na cewa 'yan Nijeriya su sa ran ganin "Ci gaba." A bayanin da ta fitar, PDP ta ce tana ra'ayin ko ma dai da wata manufa shugaban ya furta kalmar 'Ci gaba' ɗin, kada hakan ya yi nasaba da barin mulkinsa ya zuwa 29, Mayu, 2023. Ta ci gaba da cewa hasali ma 'yan Nijeriya ba su yarda da duk…
