03
Mar
Daga WAKILINMUHukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta yi kira ga Majalisar Tarayya da ta amince mata ta mayar da ƙananan guraben kaɗa ƙuri'a da ke faɗin ƙasar nan zuwa cikakkun rumfunan zaɓe. Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya yi wannan roƙon a lokacin da ya gabatar da bayani kan yadda za a sama wa masu zaɓe rumfunan kaɗa zaɓe (wato Pulling Units, PUs) a Nijeriya, a gaban Cikakken Kwamitin Majalisar Tarayya kan Hukumar Zaɓe da Al'amuran Zaɓe, a ranar Talata a Abuja. Ya ce wasu daga cikin guraben kaɗa ƙuri'ar idan aka maida su rumfunan zaɓe, za a kuma ɗauke su…
