Siyasa

Buhari ya karɓi baƙuncin Bankole da Gbenga Daniel

Buhari ya karɓi baƙuncin Bankole da Gbenga Daniel

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya karɓi bakuncin tsohon Shugaban Majalisar Wakilai, Mr Dimeji Bankole da tsohonn Gwamnan Jihar Ogun, Mr Gbenga Daniel a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja bayan da suka sauya sheƙa zuwa jam'iyyar APC. Tawagar ta ziyarci Fadar Shugaban ƙasar ne ƙarƙashin jagoranci Shugaban Kwamitin Riƙo na APC kuma gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni tare da Gwamna Abubakar Atiku Bagudu na jihar Kebbi da kuma Gwamna Mohammed Badaru na Jigawa. Da yake amsa tambayoyin manema labarai jim kaɗan bayan kammala ganawarsu, Mai Mala Buni ya ce Shugaba Buhari ya yi matuƙar farin ciki…
Read More
Jam’iyyu 18 kaɗai INEC ta sani a yanzu, inji Okoye

Jam’iyyu 18 kaɗai INEC ta sani a yanzu, inji Okoye

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa ita jam'iyyun siyasa 18 kaɗai ta sani kuma su ne za ta yi aiki da su har sai Kotun Ƙoli ta gama yanke hukunci kan jam'iyyun da aka soke rajistar su. Babban Kwamishina kuma shugaban Kwamitin Wayar da kan Masu Zaɓe da Yaɗa Labarai na hukumar, MistaFestus Okoye, shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai. A sanarwar, ya yi kira ga jam'iyyu 74 waɗanda hukumar ta soke rajistar su da su jira hukuncin na Kotun Ƙoli. Okoye ya ce, “Hukumar Zaɓe…
Read More
Imo: Kotu ta umurci INEC ta tabbatar da Ararume a matsayin wanda ya lashe zaɓen maye gurbi

Imo: Kotu ta umurci INEC ta tabbatar da Ararume a matsayin wanda ya lashe zaɓen maye gurbi

Daga WAKILINMU Wata Babbar Kotu a Abuja, ta umurci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da ta bayyana Chief Ifeanyi Ararume a matsayin wanda ya lashe zaɓen maye gurbi na mazaɓar Imo ta Arewa wanda aka gudanar ran 5, Disamb, 2020 a jihar Imo. Alƙali Taiwo Oladipupo Taiwo shi ne wanda ya yanke wannan hukunci inda ya ce kotu ta hanzarta ta tabbatar da Ararume na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen da aka gudanar. Kazalika, alƙalin ya bai wa INEC odar ta miƙa wa Ararume takardar shaidar lashe zaɓe cikin sa'o'i 72 daga lokacin da…
Read More
Jam’iyyar AAC ta fatattaki Sowore a ofishin INEC

Jam’iyyar AAC ta fatattaki Sowore a ofishin INEC

Daga FATUHU MUSTAPHA 'Ya'yan jam'iyyar African Alliance Congress (AAC) sun ce suna kan bakansu na korar da suka ce an yi wa Omoyele Sowore daga jam'iyyarsu har ma da neman 'yan sanda su kama shi saboda shigan burtun da suka ce ya yi musu. A wannan Litinin ne wani gungun mutane ƙarkashin jagorancin Sowore suka yi yinƙuri mamaye hedikwatar Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) a Abuja amma sai 'yan jam'yyar AAC ƙarƙashin jagorancin shugabansu na ƙasa, Dr. Leonard Nzenwa, suka fatattake su. Binciken Manhaja ya gano cewa, Sowore da mutanensa sun ziyarci ofishin INEC ne da nufin…
Read More
2023: Matasa sun buƙaci Tinubu ya fito takarar shugaban ƙasa

2023: Matasa sun buƙaci Tinubu ya fito takarar shugaban ƙasa

Daga WAKILINMU Mambobin Ƙungiyar Matasa Magoya Bayan Tinubu (NYMT), sun yi kira ga jigon jam’iyyar APC, Asiwaju Ahmed Tinubu, da ya fito takarar neman shugabancin ƙasa a 2023. Matasan sun yi ra’ayin cewa babu wanda ya fi cancanta ya gaji Shugaba Muhammadu Buhari kamar Tinubu domin ci gaba ƙarfafa nasararorin da gwamnatin APC ta samu. A cikin wata sanarwar manema labarai da ya fitar a Abuja, Darakta Janar na ƙungiyar, Mukhtar Husseini ya jigon ya yi sadaukarwa sosai wajen ɗorewar dimukraɗiyyar da ake cin moriyarta a yau. Ya ce buƙatar mara wa Tinubu baya ta taso ne bisa la’akari da…
Read More
Zaɓen 2019: Lauyoyi sun nemi APC ta biya su haƙƙinsu a Kano

Zaɓen 2019: Lauyoyi sun nemi APC ta biya su haƙƙinsu a Kano

Daga FATUHU MUSTAPHA Wata tawagar lauyoyi a jihar Kano ta yinƙura neman haƙƙinta daga hannun jam'iyyar APC reshen jihar na aikin da ta yi mata yayin zaɓen 2019. A wata wasiƙa da suka aika wa APC ta hannun lauyansu Usman Umar Fari, lauyoyin da lamarin ya shafa sun buƙaci jam'iyyar ta hanzarta biyansu kuɗeɗen aikin da suka yi mata yayin babban zaɓe na 2019. Lauyoyin sun ce kuɗin da suke nema a biya su, haƙƙin aikin da suka yi wa APC ne kan batutuwan da suka shafi sha'anin shari'ar zaɓe. Lauyan lauyoyin, Usman Fari, ya ja hankalin jam'iyyar kan cewa…
Read More
INEC ta buƙaci Majalisar Tarayya ta maida guraben zaɓe zuwa rumfunan zaɓe

INEC ta buƙaci Majalisar Tarayya ta maida guraben zaɓe zuwa rumfunan zaɓe

 Daga WAKILINMUHukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta yi kira ga Majalisar Tarayya da ta amince mata ta mayar da ƙananan guraben kaɗa ƙuri'a da ke faɗin ƙasar nan zuwa cikakkun rumfunan zaɓe. Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya yi wannan roƙon a lokacin da ya gabatar da bayani kan yadda za a sama wa masu zaɓe rumfunan kaɗa zaɓe (wato Pulling Units, PUs) a Nijeriya, a gaban Cikakken Kwamitin Majalisar Tarayya kan Hukumar Zaɓe da Al'amuran Zaɓe, a ranar Talata a Abuja. Ya ce wasu daga cikin guraben kaɗa ƙuri'ar idan aka maida su rumfunan zaɓe, za a kuma ɗauke su…
Read More
Gwamna Ikpeazu ya maida martani ga Sanata Adeyemi

Gwamna Ikpeazu ya maida martani ga Sanata Adeyemi

Daga WAKILINMU Gwamna Okezie Ikpeazu na jihar Abia, ya kwatanta Sanata Samrt Adeyemi na jam'iyyar APC daga jihar Kogi da mahaukaci saboda kiran sa da ya yi da mashayi. Santa Adeyemi ya kira Gwamna Ikpeazu da mashayi ne a lokacin da ya miƙe yana tofa albarkacin baki a majalisa kan batun matsalar tsaro, inda ya ce gwaman mashayi ne wanda ke cikin ɗaya daga waɗanda ba su damu da tsaron jama'arsu ba. Da yake maida martani kan batun a wajen wani taron ƙaddamar da littafi a Abuja, Ikpeazu ya ce shi dai ba ya shaye-shaye balle kuma ya zama mashayi.…
Read More
Hukumar Zaɓe za ta yi wa ma’aikatan ta bita kan aikin faɗakarwa

Hukumar Zaɓe za ta yi wa ma’aikatan ta bita kan aikin faɗakarwa

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa za ta shirya wata bita ta musamman domin wayar da kan ma'aikatan ta na sashen faɗakar da masu zaɓe da ke hedikwatar ta da kuma jihohi. Wata sanarwa da ta fito daga hukumar a ranar Asabar ta ce bitar, mai taken "Faɗakar da Mai Faɗakarwa", wato "Train-the- Trainers (ToT)", an kasa ta zuwa gida biyu saboda matsalar annobar korona (COVID-19) da ake fama da ita. Kashin farko za a yi bitar ga shugabannin sashen faɗakar da masu zaɓe (HODs VEP) da ke jihohin Kudu da kuma waɗanda su ke…
Read More