08
Sep
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin haifar da rikicin siyasa a jihar, ya kuma gargaɗi duk wani gwamna aka da ka da ya yi yunƙurin yin katsalandan a harkokin jam’iyyar PDP a jihar Ribas. Wike ya bayyana haka ne a sakatariyar jam’iyyar PDP da ke Fatakwal a ranar Asabar a yayin taron jam’iyyar na jihar. “Bari na tabbatar muku, ba yayin da muke raye ba wani zai ƙwace mana tsarin PDP. Amma bari in gaya wa mutane, na ji wasu gwamnonin suna cewa za su karɓe tsarin su mayar wa wani,…
