27
Sep
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta ƙi amincewa da buƙatar da jam’iyyar APC ta shigar na neman hana hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano, KANSIEC gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar da za a yi a ranar 26 ga watan Oktoba. Masu ƙarar su ne Aminu Aliyu Tiga da jam’iyyar APC ta hannun lauyansa, Mustapha Idris, inda su ka shigar da ƙara a ranar 18 ga watan Satumba tare da miƙa ƙorafin a ranar 20 ga watan Satumba. Su na neman kotu da ta hana KANSIEC gudanar da…
