Siyasa

Kotu ta bada umarnin sake zaɓe a mazaɓar Kakakin Majalisar Bauchi

Kotu ta bada umarnin sake zaɓe a mazaɓar Kakakin Majalisar Bauchi

Daga BASHIR ISAH Kotun Ɗaukaka Ƙara a Abuja, ta bada umarnin kan a sake gudanar da zaɓen Ningi ta Tsakiya a Ƙaramar Hukumar Ningi, Jihar Bauchi. Kakakin Majalisar Jihar Bauchi, Abubakar Suleiman, shi ne mai wakiltar Ningi ta Tsakiya a majalisar. A zaman da ta yi a ranar Juma'a, Kotun ta bada umarnin a sake zaɓe a rumfunar zaɓe guda 10 a yankin. Baturen zaɓe daga INEC, Farfesa Shuaibu Muhammad ne ya bayyana Suleiman a matsayin wanda ya lashe zaɓen da ya gudana a ranar 18 ga watan Maris, 2023. Suleiman wanda ɗan Jam'iyyar PDP ne, ya lashe zaɓe a…
Read More
Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da nasarar Gwamna Sule

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da nasarar Gwamna Sule

Daga BASHIR ISAH A ranar Alhamis Kotun Ɗaukaka Ƙara mai zamanta a Abuja ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan jihar Nasarawa inda ta tabbatar da nasarar Gwamna Abdullahi Sule a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar. A watan Oktoban da ya gabata ne Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe a jihar ta soke nasarar Gwamna biyo bayan ƙarar da Jam'iyyar PDP a jihar da ɗan takarar Ombugadu suka shigar suna ƙalubalabtar sakamakon zaɓen. Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta ce ƙaramar kotun ƙarƙashin jagorancin Ezekiel Ajayi, ta tafka kuskure a hukuncin da ta yanke musamman wajen yin amfanin da bayanan shaidu ba bisa…
Read More
Hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara: Gwamna Abba ya garzaya Kotun Ƙoli

Hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara: Gwamna Abba ya garzaya Kotun Ƙoli

Daga BASHIR ISAH Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya garzaya Kotun Ƙoli domin ƙalubalantar hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara na soke nasarar da ya samu a matsayin zaɓaɓɓen Gwamnan Kano. Wannan wata alama ce mai nuni da Gwamna Abba ba zai bari ya yi ƙasa a gwiwa bs wajen kare kujerarsa a matsayin Gwamnan Kano. Haka nan, wannan shi ne matakin kotu na ƙarshe da Yusuf zai ɗauka don kare kujerar tasa. Kwannan ne Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da hukuncin Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe, inda ta sauke Gwamna Abba na Jam'iyyar NNPP daga kujerar gwamnan Kano tare da…
Read More
Kowa ya zarce a zaɓen gwamnan Bayelsa, Imo da Kogi

Kowa ya zarce a zaɓen gwamnan Bayelsa, Imo da Kogi

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Haƙiƙa zaɓen da ya gudana a ƙarshen mako ya zama zarcewa da kowace jam'iyya da ke kan gado a jihohin. Gabanin shiga zaɓen, mun yi bayani a makon jiya na yadda a ka fara har jihohi 7 su ka zama waje da sauran jihohi a lokacin gudanar da babban zave. Sakamakon shari'un kotu su ka sauya lokutan zaɓen jihohin. Yanzu ma ba abun mamaki ba ne waɗanda ba su gamsu da sakamakon zaɓen ba su sake garzayawa kotu don neman a yi sabon lale. Nan gaba ma akwai zaɓen gwamnan jihar Edo da Ondo. Abun…
Read More
Gwamnan Binuwai ya kai bantensa a Kotun Ɗaukaka Ƙara

Gwamnan Binuwai ya kai bantensa a Kotun Ɗaukaka Ƙara

Daga BASHIR ISAH Kotun Ɗaukaka Ƙara a Abuja ta yi watsi da ƙarar da Jam'iyyar PDP a Jihar Binuwai da ɗan takarar gwamnanta, Titus Uba suka shigar. Masu ƙarar na ƙalubalantar hukuncin da Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe ta yanke ne a ranar 23 ga Satumba inda ta kori ƙarar tasu kana ta tabbatar da nasarar Hyacinth Alia na Jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar. Alƙalan kotun sun ce ƙarar ba ta darajar da za a saurare ta. Kotun ta ce PDP da ɗan takarar nata sun gaza gabatar da ƙwararan hujjoji don kare zargin amfani da…
Read More
PDP ta lashe zaɓen ƙananan hukumomi a Taraba

PDP ta lashe zaɓen ƙananan hukumomi a Taraba

Daga BASHIR ISAH Jam'iyyar PDP a Jihar Taraba ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a jihar kwanan nan. A ranar Lahadin da ta gabata Hukumar Zaɓe ta Jihar Taraba, TSIEC, ta bayyana cewa PDP ce ta lashe zaɓen ciyamomi a ilahirin ƙananan hukumomi 16 da jihar ke da su, kana ta samu kansiloli guda 168. Shugaban hukumar zaɓen jihar, Dr. Philip Duwe, shi ne ya bayyana sakamakon zaɓen a Jalingo, babban birnin jihar, inda ya ce shida daga cikin jam'iyyu 19 da aka yi wa rijista ne suka shiga zaɓen. Dr Duwe ya yaba wa 'yan jarida bisa…
Read More
APC, zaɓe ko naɗi?

APC, zaɓe ko naɗi?

Ban ce jam'iyya mai mulki APC na da tasirin mamaye duka faɗin ƙasarmu ba. Amma dai ga alamu har yanzu ta na da tasiri wajen samun magoya baya idan ta je zaɓe. Zaɓen ranar 11/11/2023 wanda aka gudanar a jihohin Bayelsa, Kogi, Imo tun kafin aje ranar ban hango ma APC rasa jihohin duka ba musamman yadda sau da dama ta ke ƙoƙari wajen nemo 'yan takara fitattu masu jama'a ta tsayar wanda ta hakan ta ke shammatar jam'iyyun adawa aje zaɓe su zamo yan kallo. Mu kula da kyau, har kullum ita siyasa abu ce mai buƙatar zurfafa tunani…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta sauke Gwamnan Filato

Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta sauke Gwamnan Filato

Daga BASHIR ISAH Kotun Ɗaukaka Ƙara ta soke Caleb Muftwang na PDP a matsayin halastaccen zaɓaɓɓen Gwamnan Jihar Filato sannan ta ayyana Dr Nentawe na Jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓe. Kotun ta yanke hukuncin ne a zaman da ta yi a wannan Lahadin. Alƙalan kotun ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Williams-Dawodu, sun ayyana ɗan takarar Jam'iyyar APC, Dr. Nentawe Yilwatda, a matsayin halastaccen wanɗa ya lashe zaɓen. Kotun ta umarci Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), da ta janye shahadar lashe zaɓen da ta miƙa wa Mutfwang sannan ta miƙa wa Dr. Yilwatda.
Read More
Shugaban Ƙaramar Hukumar Bade ya yaba wa Buni bisa romon dimukraɗiyya da ya samar a Yobe

Shugaban Ƙaramar Hukumar Bade ya yaba wa Buni bisa romon dimukraɗiyya da ya samar a Yobe

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Ƙaramar Hukumar Bade a Jihar Yobe, Alhaji Ibrahim Baba Gana, ya yaba wa Gwamna Mai Mala Buni bisa romon dimukraɗiyya da ya samar wa al'ummarsa tun daga 2019 zuwa yau, inda ya kwatanta shi da mutum mai tsananin kishin al'ummarsa da jiharsa. Honorabul Ibrahim Baba Gana ya ce Maigirma Buni ya samu nasarori wajen ciyar da Jihar Yobe gaba, inda ya ce a cikin shirye-shiryensa ya ƙarfafa wa masu ƙaramin ƙarfi da jari da kuma tallafa wa gidajen marayu, samar da ayyukan yi ga matasa masu tasowa a faɗin ƙananan hukumomin, ƙaramar hukumar…
Read More
Gwamnan Bauchi ya kai bantensa a shari’ar Kotun Ɗaukaka Ƙara

Gwamnan Bauchi ya kai bantensa a shari’ar Kotun Ɗaukaka Ƙara

Daga BASHIR ISAH Kotun Ɗaukaka Ƙara mai zamanta a Abuja ta tabbatar da nasarar Bala Abdulkadir Mohammed a matsayin Gwamnan Jihar Bauchi. Hukumar INEC ce ta bayyana Mohammed a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan da ya gudana ran 18 ga Maris, inda daga bisani babban abokin hamayyarsa na Jam'iyyar APC, AVM Sadique Abubakar (rtd), ya ƙi amicewa da sakamakon zaɓen ya garzaya Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe. Duk da dai Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen ta yanke hukuncin Mohammed ne halastaccen zaɓaɓɓen gwamnan Bauchi, amma hakan bai hana Abubakar garazayawa Kotun Ɗaukaka Ƙara ba. A zaman da Kotun ta yi a…
Read More