Siyasa

Kotun Ƙoli ta ɗage yanke hukunci kan zaɓen Gwamnan Kano

Kotun Ƙoli ta ɗage yanke hukunci kan zaɓen Gwamnan Kano

Daga BASHIR ISAH Kotun Ƙoli ta ɗage yanke hukuncin zaɓen gwamnan Kano zuwa wani lokaci da ba ta ambata ba. Zaman da Kotun ta yi mai alƙalai biyar a ranar Alhamis, ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Inyang Okoro. A ranar 17 ga Nuwamban 2023 Gwamnan Kano, Abba Yusuf da Jam'iyyarsa ta NNPP suka ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ƙoli inda suke ƙalubalantar hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara da ta soke nasarar da Gwamna Abba ya samu a zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ran 19 ga Maris. Kazalika, jam'iyyar ta nusar da Kotun Ƙolin dambarwar da ta auku a hukuncin…
Read More
Lalong ya sha rantsawar zama Sanatan Filato ta Kudu

Lalong ya sha rantsawar zama Sanatan Filato ta Kudu

Daga BASHIR ISAH An rantsar da tsohon Gwamnan Jihar Filato, Simon Lalong, a matsayin sanata mai wakiltar Filato ta Kudu a Majalisar Dattawan Nijeriya. Lalong ya yi murabus ne daga muƙamin Ministan Ƙwadago a gwamnatin Tinubu sannan ya maye gurbin Napoleon Bali na Jam'iyyar PDP wanda Kotun Ɗaukaka Ƙara ta sauke shi biyo bayan ƙarar da Lalong ya shigar a kansa a kotun sauraren ƙararrakin zaɓe. Akawun majalisar, Chinedu Akubueze, shi ne ya rantsar da Long yayin zaman majalisar a ranar Laraba ƙarƙashin jagorancin Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio. Da yake jawabi jim kadan bayan rantsar da Lanlon a matsayin…
Read More
Fabrairu INEC za ta sake zaɓen wasu mazaɓu da na cike-gurbi – Shugaban INEC

Fabrairu INEC za ta sake zaɓen wasu mazaɓu da na cike-gurbi – Shugaban INEC

Daga BASHIR ISAH Ya zuwa watan Fabrairu na baɗi Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ke sa ran sake zaɓuɓɓuka a wuraren da akwai buƙatar haka a sassan ƙasa. Shugaban hukumar na ƙasa, Mahmoud Yakubu, shi ne ya bayyana haka a wajen taron da suka yi da jam'iyyum siyasa a ranar Litinin. “Game da zaɓen cike gurbi, idan ba a manta ba a jawabin da na yi a lokacin rantsar da Kwamishinonin Zaɓe (RECs) haɗe da taron zangon ƙarshe da muka yi da baƙi ɗaya kwamishinonin zaɓe na ƙasa, na ce hukumar za ta gudanar da zaɓe domin cike guraben da…
Read More
’Yan bindiga sun wawashe takardun kotun zaɓen gwamnan Kogi

’Yan bindiga sun wawashe takardun kotun zaɓen gwamnan Kogi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wasu 'yan bindiga sun kai hari kan magatakardan Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓen gwamnan Jihar Kogi, David Umar Mike, tare da kwashe takardun masu ƙara. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar (PPRO), SP William Aya, ya bayyana hakan a Lokoja ranar Laraba. Hukumomin 'yan sandan sun ce maharan da suka kai harin na sakatariyar kotun sauraron ƙararrakin zaɓen gwamnan jihar sun kwashe dukkanin takardun ƙarar da wasu jam’iyyun siyasa biyar suka shigar. A cewar hukumomin ’yan sanda, takardun da aka kwace daga hannun Mike sun haɗa da, ƙorafe-ƙorafen da jam’iyyu huɗu (4): Action Alliance…
Read More
Rashin adalci a shari’ar zaɓen Kano na iya haddasa tashin hankali – NNPP

Rashin adalci a shari’ar zaɓen Kano na iya haddasa tashin hankali – NNPP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar adawa ta NNPP a Nijeriya ta ce hana ta ƙwace mata zaven da ta ci a jihar Kano, zai iya janyo tashin hankalin da zai yaɗu zuwa sauran ƙasahen Afirka. Wata sanarwa da muƙaddashin shugaban jam'iyyar na ƙasa, Abba Kawu Ali, ya fitar, kuma babban jami'i mai binciken kuɗi na jam'iyyar, Ladipo Johnson ya karanta a gaban ofisoshin jakadancin Ƙasashen Yamma ranar Laraba, NNPP ta yi iƙirarin cewa akwai alamun da ke nuna cewa ana yunƙurin yi wa zaɓen mafi rinjayen al'ummar Kano zagon ƙasa. 'Ya'yan jam'iyyar suna ci gaba da zanga-zanga a…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: An naɗa sabon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa

Da Ɗumi-ɗumi: An naɗa sabon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa

Daga BASHIR ISAH 'Yan Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa sun zaɓi Danladi Jatau a matsayin sabon Kakakin da zai ci gaba da jagorancin majalisar. A ranar Juma'a aka naɗa Jatau a matsayin sabon shugaban majalisar jihar biyo bayan tsige Ibrahim Balarabe Abdullahi da Kotun Ɗaukaka Ƙara mai zamanta a Abuja ta yi daga kujerasa. Kazalika, 'yan majalisar sun naɗa Mohammed Oyanki a matsayin Mataimakin Kakakin majalisar. Jatau na wakiltar shiyyar Kokona ne a majalisar, yayin da Oyanki ke wakiltar mazaɓar Doma ta Arewa.
Read More
2024: Babu abin da zai dakatar da ni daga takarar Gwamnan Edo – Shaibu

2024: Babu abin da zai dakatar da ni daga takarar Gwamnan Edo – Shaibu

Daga BASHIR ISAH Mataimakin Gwnan Jihar Edo, Philip Shaibu, ya bayyana aniyarsa ta neman shiga takarar gwamnan jihar ya zuwa 2024. Ya ce zai tsaya takarar ne a ƙarƙashin Jam'iyyar PDP, tare da cewa, babu abin da zai hana shi neman kujerar gwamnan jihar. Shaibu ya bayyana aniyyar tasa ce da safiyar ranar Litinin a cibiyar Biohop Kelly Centre da ke Benin City, babban jihar. Da yake yi wa dandazon masoyansa jawabi, Shaibu ya ce a matsayinsa na ɗan asalin jihar wanda kuma ya san ciwon al'ummar jihar, zai nemi shugabancin jihar ne don cigabanta da ma al'ummarta baki ɗaya.…
Read More
Shari’ar kotunan Nijeriya ta zama tufka da warwara – PDP

Shari’ar kotunan Nijeriya ta zama tufka da warwara – PDP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babbar jam'iyyar adawa ta PDP a Nijeriya, ta bayyana hukunce-hukuncen da kotunan ɗaukaka qara suka yi, inda suka ƙwace nasarar wasu gwamnoni a matsayin "karan-tsaye" ga dimokraɗiyya. Jam'iyyar adawar na zargin APC mai mulkin Nijeriya ne da "amfani da qarfin iko" wajen tanqwara hukuncin kotunan, zargin da APC ta musanta. "Shari'ar Nijeriya ta zama kamar rawar 'yan mata yanzu; idan an yi gaba, sai a koma baya," inji Mataimakin Sakataren PDP na Ƙasa, Ibrahim Abdullahi. Ya ce dalilan da mutanen nan ke gabatarwa suna kwace zaɓen nan, akasari batutuwan da suka shafi kafin zaɓe…
Read More
Muna maraba da kafa jam’iyyar haɗaka kamar yadda Atiku ya nema – NNPP

Muna maraba da kafa jam’iyyar haɗaka kamar yadda Atiku ya nema – NNPP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam'iyyar adawa ta NNPP a Nijeriya ta nuna aniyarta ta shiga jam'iyyar haɗaka da sauran jam'iyyun adawa kamar yadda Atiku Abubakar ya nema a makon da ya gabata. Ɗan takarar na jam'iyyar PDP a zaven shugaban Nijeriya na 2023, Atiku ya zargi APC da yunƙurin mayar da Nijeriya bin tsarin jam'iyya ɗaya sannan ya yi kira ga jam'iyyun adawa da su dunqule don yin waje da jam'iyyar mai mulki. Shugaban Riƙo na NNPP na Ƙasa, Abba Kawu Ali, ya faɗa a yau Talata yayin wani taron manema labarai cewa kiran na Atiku abin a…
Read More
APC zaɓe ko ƙwace?

APC zaɓe ko ƙwace?

Ga dukkan alamu jam'iyya mai mulki APC tana daf da kwace duk kujerun gwamnonin arewa. Jihar Kano ce ta farko wajen yiwuwar ta zamo ta APC amma idan Kotun Ƙoli ta tabbatar da hakan. Sai jihar zamfara wacce ga alamu sai an sake zaɓe a wasu yankuna a tsakani gwamnan PDP mai karagar mulki da kuma tsohon gwamna na APC wanda minista ne a yanzu. Jihar Filato ma a cen kotu ta kwace kujera ta gwamnan PDP ta mayar ga gwamnan APC wanda su kai takara. Amma mu kula da kyau? Dukkanin inda a ke ƙwace kujeru na gwamnoni ko…
Read More