21
Dec
Daga BASHIR ISAH Kotun Ƙoli ta ɗage yanke hukuncin zaɓen gwamnan Kano zuwa wani lokaci da ba ta ambata ba. Zaman da Kotun ta yi mai alƙalai biyar a ranar Alhamis, ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Inyang Okoro. A ranar 17 ga Nuwamban 2023 Gwamnan Kano, Abba Yusuf da Jam'iyyarsa ta NNPP suka ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ƙoli inda suke ƙalubalantar hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara da ta soke nasarar da Gwamna Abba ya samu a zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ran 19 ga Maris. Kazalika, jam'iyyar ta nusar da Kotun Ƙolin dambarwar da ta auku a hukuncin…
