Wasanni

Real Valladolid ta zargi Man City da zuga Bah ya soke kwantiraginsa

Real Valladolid ta zargi Man City da zuga Bah ya soke kwantiraginsa

Real Valladolid ta zargi Manchester City da ƙarfafa gwiwa ga ɗaya daga ’yan wasanta, domin ya soke yarjejeniyarsa ya koma buga gasar firimiyar Ingila. Mai tsaron baya, Juma Bah ya sanar da ƙungiyar ta Sifaniya ranar Talata cewar yana so ya katse yarjejeniyarsa, saboda ya koma Manchester City kan kankanin kuɗi. Tun a baya City ta nemi izinin Valladolid, domin tattaunawa kan sayen matashin mai shekara 18, domin ya koma taka leda a Etihad. Bah bai halarci atisaye ba ranar Laraba, inda hukumar ƙwallon ƙafar Sifaniya ta tabbatar cewar ya biya sauran ƙunshin kwantiraginsa a ƙungiyar, domin ya kara gaba.…
Read More
Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Inter Milan da Borussia Dortmund na ƙyalla ido kan ɗan wasan tsakiya na Ingila, Jack Grealish mai shekara 29, ganin cewa babu tabbas game da ci gaba da zaman shi a Manchester City. AC Milan na tunanin ɗaukar aron ɗan wasan gaba na Manchester United, Rasmus Hojland mai shekara 21 a duniya da kuma Joshua Zirkzee mai shekara 23. Juventus ta tattauna da Udinese kan sayen ɗan wasa Thomas Krintensen mai shekara 23, wanda Tottenham da Leicester City ke ƙyalla ido a kansa. Napoli na fatan za ta cimma yarjejeniyar fam miliyan 50 domin ɗauko ɗan wasan gefe na Manchester…
Read More
Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Hada-hadar kasuwar ’yan wasan ƙwallon ƙafa

Chelsea ta karbi tayi kan ɗan wasanta mai shekara 28, Ben Chilwell, wanda sau guda ya taka mata leda a wannan kakar. Arsenal ta tura wakilai domin sa ido kan ɗan wasan gaba a Atalanta mai shekara 25 asalin ƙasar Italiya, Mateo Retegui. Rashin jituwa tsakanin kocin AC Milan, Paulo Fonseca da ɗan wasan Faransa mai tsaron baya, Theo Hernandez na iya sa ɗan wasan mai shekara 27 ya bar San Siro yayin da Real Madrid da Manchester United ke zawarcinsa. Tottenham ta nuna kwaɗayinta kan ɗan wasan Atalanta da Ingila, Ben Godfrey mai shekara 26, a yarjejeniyar gajeren lokaci.…
Read More
Moroko za ta sake karɓar baƙuncin AFCON a 2026

Moroko za ta sake karɓar baƙuncin AFCON a 2026

Moroko za ta sake karɓar baƙuncin kofin Afrika na Mata WAFCON karo na uku a jere a 2026, yayin da aka sanar da wasannin share fagen shiga gasar a ranar Alhamis kuma ƙasashe 38 ne za su fara fafatawa a gasar, an samu ragin ƙasashe huɗu da za su buga gasar 2024. Kowacce ƙasa za ta buga wasa biyu, gida da waje, domin samun 11 da za su hadu da mai masaukin baƙi su buga gasar WAFCON ta 2026, sannan ƙasashe shida da ke saman jerin jadawalin Afrika da suka haɗa da Nijeriya da South Africa da Ghana da Cameroon…
Read More
Sauya shaidar zama ɗan ƙasa zuwa Nijeriya ne mabuɗin samun nasara ta – Lookman

Sauya shaidar zama ɗan ƙasa zuwa Nijeriya ne mabuɗin samun nasara ta – Lookman

Dan wasan gaba na Nijeriya Ademola Lookman ya ce sauya shaidar zama ɗan ƙasa daga Ingila zuwa Super Eagles ta Nijeriya a shekarar 2022 ita ce mabuɗin nasarar da yake samu a yanzu. Lookman, wanda aka haife shi a Landan kuma ya wakilci zakarun a matakin ƙasa da shekaru 17, inda ya taimaka musu lashe gasar kofin duniya na ƙungiyoyi masu shekaru, ya yarda cewa shawarar sauya sheƙa zuwa Nijeriya ta sauya rayuwarsa. "Ina tsammanin tun lokacin da na sanya rigar Super Eagles, ya kasance mai amfani," inji Lookman a SportyTV. "Mun sami damar cimma nasara da yawa a ƙungiyance…
Read More
Manchester United za ta yi musanyar Osimhen da Rashford

Manchester United za ta yi musanyar Osimhen da Rashford

Napoli ta bai wa Manchester United damar sayen Victor Osimhen a watan Janairu kuma a shirye take don musayar 'yan wasa don sauƙaƙe cinikin. Dan wasan na Nijeriya, wanda a halin yanzu yake zaman aro a Galatasaray, ya taka rawar gani sosai, inda ya zura ƙwallaye tara a wasanni 11 na ƙasar Turkiyya. Buƙatar Man United na samun amintaccen lamba tara ya ƙaru a ƙarƙashin kocin Ruben Amorim, inda Marcus Rashford, Rasmus Hojlund, da Joshua Zirkzee ke fafutukar lambar. Yayin da ake neman sa hannun Osimhen, matsalolin kuɗi na iya dagula yunƙurin. Rashford, Hojlund, da Zirkzee suna samun haɗakar fam…
Read More
Dalilan da suka sa Man City ta kasa kataɓus a kakar bana

Dalilan da suka sa Man City ta kasa kataɓus a kakar bana

Yanzu haka ƙungiyar Manchester City ta ƙasar Ingila tana cikin wani yanayi maras tabbas a gasar Firimiyar Ingila kuma babu wata alamar sassauci a nan kusa. Rashin nasarar da ta samu a ranar Asabar a hannun Aston Aɓilla 2-1 ya sa sun sauka daga 'yan huɗun farko cikin wasa takwas da ta buga. Saouthanmpton ce kaɗai ta fi Man City yawan wasannin da babu nasara cikin yawan wasannin, amma kuma idan ta samu maki ɗaya a wasanta na gaba bayan naɗa sabon koci Iɓan Juric, za ta kamo City a yawan maki. Hatta Wolves - da ta kori kocinta Gary…
Read More
Uwa da ’yarta sun lashe gasar tseren gudu a Kaduna

Uwa da ’yarta sun lashe gasar tseren gudu a Kaduna

Wata dattijuwa da ’yarta mai shekara 17 sun lashe gasar tseren gudu a bikin raya al’adun al’ummar Kudancin Jihar Kada (SKFEST) ta bana. Dattijuwa Elizabeth Nuhu Bawa ce ta zama Gwarzuwa a yayin da ’yarta, Grace, ta zo ta biyu a gasar. ’Yan tsere da dama ne suka kwashinsu a hannun dattijuwa Elizabeth da ’yarta Garda a gasar fa aka fafata a filin wasa na garin Kafanchan. Grace mai shakara 17 ta ce ta so a ce ta doke mahaifiyarta domin ta zo ta ɗaya amma mahaifiyar ta fi ta kuzari. Amma duk da haka ta ce tana fatan nan…
Read More
Usyk ya sake doke Fury tare da riƙe kambinsa

Usyk ya sake doke Fury tare da riƙe kambinsa

Watanni bakwai bayan nasararsa ta farko, Oleksandr Usyk ɗan ƙasar Ukraine ya sake doke ɗan ƙƙsar Birtaniya Tyson Fury a ranar Asabar a birnin Riyadh, abin da ya sa ya ci gaba da riƙe matsayinsa bayan kare duka kambinsa na WBA da WBC da WBO.  Oleksandr Usyk ɗan ƙasar Ukrainian mai shekaru 37, ya nuna bajintarsa wajen taɓa Fury sau da yawa tare da doke shi da hannun hagu, abin da ya sa duka alƙalai ukun suka amince da ya samu maki 116-112, sannan ya ci gaba da zama ba'a yi nasara a kansa ba a fafatawar 23. Da wannan…
Read More
Saka zai yi jinyar makonni – Arteta

Saka zai yi jinyar makonni – Arteta

Kocin Arsenal Mikel Arteta ya ce ɗan wasan gaba Bukayo Saka ba zai buga wasa tsawon makonni masu yawa saboda rauni a bayan gwiwarsa. An fitar da ɗan wasan na Ingila a wasan da Arsenal ta doke Crystal Palace 5-1, inda ya bar filin wasa na Selhurst Park da sanduna. Saka mai shekara 23 ya ci wa Arsenal ƙwallo tara kuma ya bayar aka ci 13 cikin wasa 24 da ya buga mata a dukkan gasanni. "Lamarin babu kyau. Zai yi jinyar makonni masu yawa," inji Arteta. "Haka dai lamarin yake. Ya ji rauni, ba zamu iya sauya komai ba.…
Read More