25
Jan
Real Valladolid ta zargi Manchester City da ƙarfafa gwiwa ga ɗaya daga ’yan wasanta, domin ya soke yarjejeniyarsa ya koma buga gasar firimiyar Ingila. Mai tsaron baya, Juma Bah ya sanar da ƙungiyar ta Sifaniya ranar Talata cewar yana so ya katse yarjejeniyarsa, saboda ya koma Manchester City kan kankanin kuɗi. Tun a baya City ta nemi izinin Valladolid, domin tattaunawa kan sayen matashin mai shekara 18, domin ya koma taka leda a Etihad. Bah bai halarci atisaye ba ranar Laraba, inda hukumar ƙwallon ƙafar Sifaniya ta tabbatar cewar ya biya sauran ƙunshin kwantiraginsa a ƙungiyar, domin ya kara gaba.…
