Wasanni

Ƙasashen da suka yi fice a fagen ƙwallon ƙafa a duniya

Ƙasashen da suka yi fice a fagen ƙwallon ƙafa a duniya

A jerin ƙasashen da suka yi fice a fagen wasan ƙwallon aafa, ƙasar Brazil ce a sahun gaba, Belgium ta biyu, Argentina ta uku, Faransa ta huɗu, Ingila ta biyar, Sifaniya ta shida, Italiya ta bakwai, Netherland ta takwas, Portugal ta tara, a yayin da ƙasar Denmark ta zo matsayi na goma, a cewar hukumar FIFA. Hukumar ta kuma ce a ƙasashen Afrika, asar Senegal ita ce ta shatakwas a fagen tamaula a duniya, sai Morocco ta ashirin da biyu, Tunisia ta talatin, Nijeriya ta talatin da ɗaya, Kamaru ta talatin da takwas, Masar ta arba'in, sai kuma Algeria ta…
Read More
Manyan ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa da suka fi yawan lashe kofuna a duniya

Manyan ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa da suka fi yawan lashe kofuna a duniya

Manyan ƙungiyoyin ƙwallon kafa na Turai sune ƙungiyoyin da aka fi sanin su a duniya kuma suna jan hankalin magoya bayansu daga ko'ina a faɗin duniya. Za mu yi dubi ne kan ƙungiyoyin da suka fi lashe kofuna da kuma inda suka fi samun nasara, a cikin gida ko kuma a ƙasashen waje. Bayan nishaɗi, tarihin ƙwallon ƙafa ya rubuta masu nasara kuma akwai ƙungiyoyi kaɗan da suka yi fice. Waɗannan su ne ƙungiyoyi 10 da ke da mafi yawan lashe kofuna a duniya har zuwa Yuni 2022. 1. Nacional (Uruguay): Tawagar Uruguay ita ce ta fi samun nasara a…
Read More
Nani ya rataye takalmansa daga wasa ƙwallon ƙafa

Nani ya rataye takalmansa daga wasa ƙwallon ƙafa

Nani ya sanar da yin ritaya daga taka leda a matakin ƙwararren ɗan wasa mai shekara 38. Tsohon ɗan wasan Manchester United ya rataye takalmansa a Club Estrela Amadora da ke garinsu. Dan ƙasar Portugal ya buga tamaula a babbar gasar ƙwallon ƙafa ta Turkiya da Sifaniya da Italiya da Australia da kuma Amurka. Sir Aleɗ Ferguson ne ya ɗauko Nani a 2007 daga Sporting ta Portugal, an kuma sanar da magoya bayan United sayen ɗan ƙwallon tare da Anderson a ranar. Nani ya bayar da gudunmuwar da United ta lashe Premier League huɗu, ya taka rawar gani da ƙungiyar…
Read More
Odegaard ya ɗaura ƙyallen kyaftin karo na 100 a Arsenal

Odegaard ya ɗaura ƙyallen kyaftin karo na 100 a Arsenal

Arsenal za ta je gidan Fulham, domin buga Premier League wasan mako na 15 da za su kara ranar Lahadi a Craɓen Cottage. Idan har Martin Odegaard ya shiga wasan zai zama karo na 100 da zai ja ragamar Gunners a matakin ƙyaftin. Haka kuma wasa na 163 da mai shekara 25 zai yi wa Gunners, tun bayan da ya koma Emirates da taka leda daga Real Madrid. Odegaard ya fara ɗaura ƙyallen ƙyaftin ɗin Arsenal a wasa da Southampton a cikin watan Maris a 2022. Cikin ƙididdigar da aka yi, ɗan ƙasar Norway, an ci wasa 66 tare da…
Read More
Bayern ta yi wasa biyar cikin nasara a Bundesliga

Bayern ta yi wasa biyar cikin nasara a Bundesliga

Bayern Munich ta yi wasa na biyar a jere ba tare da rashin nasara ba, bayan da ta doke Heidenheim 4-2 ranar Asabar a Bundesliga. Jamal Musiala ne ya ci biyu, sai Dayot Upamecano da Leon Goretzka da kowanne ya zura ɗaya a raga. Ita kuwa Heidenheim ta ci biyu ne ta hannun Honsak da kuma Dorsch. Bayern ta fara wannan ƙwazon tun bayan da ta doke Bochum 5-0 ranar 27 ga watan Oktoba a babbar gasar tamaula ta Jamus. Da wannan sakamakon Bayern ta ci gaba da zama ta ɗaya a kan teburin Bundesliga da tazarar maki shida tsakani…
Read More
FIFA ta fitar da jadawalin Gasar Kofin Duniya ta ƙungiyoyi

FIFA ta fitar da jadawalin Gasar Kofin Duniya ta ƙungiyoyi

Hukumar ƙwallon ƙafar Duniya (FIFA), ta fitar da jadawalin Gasar Kofin Duniya da za a doka. An sanya ƙungiyar Palmeiras ta ƙasar Brazil da takwararta ta ƙasar Portugal Porto a rukunin “A” tare da ƙungiyar Inter Miami ta jagoran kofin duniya dan ƙasar Argentina Messi wanda FIFA ta bata gurbi bayan da ta yi zarra a gasar MLS ta wannan kakar. Lionel Messi da ƙungiyar Inter Miami za su ƙaddamar da gasar cin kofin duniya ta ƙungiyoyi 32 da Hukumar ƙwallon ƙafar Duniya (FIFA) ta ƙirƙira, lokacin da babbar ƙungiyar ƙwallon ƙafar za ta haɗu da takwararta ta ƙasar masar…
Read More
Amorim ya kafa tarihin samun nasara a wasansa na farko a Manchester United

Amorim ya kafa tarihin samun nasara a wasansa na farko a Manchester United

Amorim ya zama kocin Man United na farko a wasan firimiya a gida da ya ci ƙwallo sama da biyu, karon farko da Man United ta zura 4-0 a bana a gasar. Manchester United ta doke Everton 4-0 a wasan mako na 13 a gasar Firimiya da suka kara ranar Lahadi a Old Trafford. Marcus Rashford ne ya fara cin ƙwallo tun kan hutu, na shida da yake da hannu a cin Everton daga karawa ta takwas kenan. Bayan da suka koma zagaye na biyu Man United ta ƙarasa zura uku a raga ta hannun Joshua Zirkzee, sannan Rashford ya…
Read More
Za mu dawo kan ganiyarmu idan ’yan wasanmu suka murmure – Guardiola

Za mu dawo kan ganiyarmu idan ’yan wasanmu suka murmure – Guardiola

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, ya ce za su sake dawowa ganiyarsu idan har duka 'yan wasansa suka kammala murmurewa. Da dama daga cikin ’yan wasan ƙungiyar na Man City sun sha fama da rauni, musamman zakarar kyautar Ballon d’Or Rodri da Kyle Walker da Jack Grealish da Kevin De Bruyne da Mateo Kovacic sai kuma Ruben Dias. Wannan rauni ya sanya Man City ta samu mummunar koma baya a wannan kaka, musamman ma yadda ta yi kunnen doki daya a cikin wasanni 7 na baya-bayan da ta yi a dukkanin gasannin da take fafatawa, sannan ta yi rashin nasara…
Read More
CHAN 2025: Super Eagles ta gayyaci ’yan wasan Kano Pillars uku

CHAN 2025: Super Eagles ta gayyaci ’yan wasan Kano Pillars uku

Kocin Super Eagles, Austin Eguavon ya gayyaci ’yan Kano Pillars uku ciki har da Rabi'u Ali, domin karawa da Ghana a neman shiga gasar CHAN 2025. Sauran da aka kira daga Pillars sun haɗa da Abiam Nelson da kuma Adams Aminu Sani a tawagar ta Super Eagles masu taka leda a gida. Rabi'u Ali yana kan ganiya a wasannin firimiyar Nijeriya ta bana, wanda ya zura ƙwallo takwas a raga, bayan kammala wasannin mako na 15. Ana sa ran ’yan wasan da aka gayyata za su je katafaren filin wasa na Remo Stars a Ikenne da ke jihar Ogun daga…
Read More
Lampard ya zama sabon kocin Coventry City

Lampard ya zama sabon kocin Coventry City

An naɗa tsohon ɗan wasan tsakiya na ƙungiyar ƙwallon ƙafar Chelsea da ƙasar Ingila Frank Lampard ya zamo kocin Coventry a bisa yarjejeniyar shekaru 2 da rabi. Lampard ya maye gurbin Mark Robins, wanda aka sallama a farkon wannan watan. Coventry na mataki na 17 a gasar zakarun bayan wasanni 17 inda suka yi rashin nasara a wasanninsu 4 na karshe. A matsayinsa na ɗan wasa, Lampard ya ciwa Chelsea ƙwallaye 211 a dukkanin gasar da ta buga a shekaru 13 da ya shafe a cikinta masu cike da daukar kofi. Ya taɓa horar da ƙungiyoyin Chelsea da Everton a…
Read More