11
Mar
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Bayern Munich ta kawo ƙarshen fatan PSG na lashe kofin zakarun Turai cikin wannan kaka, bayan da ta lallasata da ƙwallaye biyu da nema a wasansu na daren ranar Laraba. Tun a haɗuwar farko dama Bayern Munich ta lallasa PSG da ƙwallo 1 mai ban haushi har gidanta cikin watan jiya, gabanin nasarar ta daren ranar wanda ke nuna tauraruwar ta Jamus ta doke zakarar ta Faransa da ƙwallaye 3 da nema a jumlace. Cikin shekaru 11 da PSG ta shafe ta na fafutukar ganin ta lashe kofin na zakarun Turai, wannan…