Wasanni

Aston Villa ta cimma yarjejeniyar ɗaukar Duran

Aston Villa ta cimma yarjejeniyar ɗaukar Duran

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Aston Villa ta cimma yarjejeniyar ɗaukar ɗan ƙwallon tawagar Colombia, Jhon Duran daga Chicago Fire. Duran, mai shekara 19, ya ci ƙwallo takwas ya kuma bayar da shida aka zura a raga a wasa 28 da ya yi wa Chicago. Kammala yarjejeniyar ta alakanta idan an auna koshin lafiyar ɗan wasan, sannan idan ya samu takardar shaidar aiki a Burtaniya. Ɗan ƙwallon zai yi takara a gurbi ɗaya da Ollie Watkins da Danny Ings a ƙungiyar da Unai Emery ke jan ragama, bayan da 'yan wasan biyu suka ci ƙwallo bakwai a tsakaninsu. Duran ya buga…
Read More
A karon farko za a fara haska wasannin gasar Saudiyya a tashar DSTV

A karon farko za a fara haska wasannin gasar Saudiyya a tashar DSTV

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Bayan naɗa Cristiano Ronaldo a matsayin sabon ɗan wasan ƙungiyar Al Nassr ta ƙasar Saudiyya, hukumar gasar sun ƙulla yarjejeniya da DSTV don yaɗa wasannin gasar Larabawa a tashar DSTV. Za a nuna gasar Larabawa ta talabijin a Channel 240. Kowa zai iya kallon wasannin Al Nassr a tashar 240. Wannan shi ne karo na farko a tarihi da za a nuna gasar wasannin Asiya ta talabijin a tashar DSTV. A ɗaya ɓangaren kuma, Hukumomin Saudiyya na shirin kau da kai daga dokokin auratayya ta ƙasar domin yarjewa sabon tauraron ɗan wasan da ƙungiyar Al Nassr…
Read More
Yanayin albashin Messi idan Al-Hilal ta samu nasarar saye shi

Yanayin albashin Messi idan Al-Hilal ta samu nasarar saye shi

Ga yadda albashin Lionel Messi zai kasance idan kulob ɗin Al-Hilal ta samu nasarar saye shi: Shekara: Biliyan N161.8 Wata: Biliyan N13.4 Mako: Biliyan N3.3bn Rana: Miliyan N481.7 Awa: Miliyan N20.7 Manhaja ta rawaito ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Al-Hilal da ke Saudiyya na zawarcin ɗan wasan inda ta ce a shirye take ta biya shi Dalar Amurka miliyan 385 kwatankwacin biliyan N161.8 duk shekara.
Read More
Al-Hilal na zawarcin Messi kan biliyan N161.8 a shekara

Al-Hilal na zawarcin Messi kan biliyan N161.8 a shekara

Daga BASHIR ISAH Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Saudiyya, wato Al-Hilal, na zawarcin gwarzon ɗan wasan nan na Argentina, Lionel Messi kan kuɗi Dalar Amurka miliyan 385, kwatankwacin Naira biliyan 161.8. Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan da babbar abokiyar hamayyar Al-Hila ɗin, wato Al-Nassr ta saye shahararren ɗan wasan nan Cristiano Ronaldo. Da alama dai, Saudiyya ta ba da himma wajen ganin ta mallake gwarazan da ake ji da su a duniyar ƙwallon ƙafa. Domin saye Messi, dole Al-Hilal ta yi aman Dala miliyan $385, farashin da ake ganin ba kowa zai iya biya a kan ɗan wasan ba.…
Read More
Saudiyya ta halasta wa Ronaldo zaman daduro da farkarsa

Saudiyya ta halasta wa Ronaldo zaman daduro da farkarsa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Bayan amsar Cristiano Ronaldo a matsayin sabon ɗan wasan ƙungiyar Al Nassr ta ƙasar Saudiyya, hukumomin ƙasar za su sahale masa cigaba da zaman daduro da budurwarsa, Georgina Rodriguez, duk da cewa, hakan ya saɓa da dokokin ƙasar, waɗanda suka dace ds Shari'ar Musulunci. Haka nan, hukumar gasar ƙasar ta ƙulla yarjejeniya da tauraron DSTV, don yaɗa wasannin gasar ƙasar a tashar DSTV sakamakon taka leda da Ronaldo zai fara yi a gasar wasannin ƙwallon ƙafa na ƙasar. Za a riƙa nuna gasar ne a tashar ta talabijin ta DSTV ɗin mai lamba 240. Wato kowa…
Read More
’Yan wasan Kamaru 32 sun gaza tsallake gwajin shekarun ‘yan ƙasa da 17

’Yan wasan Kamaru 32 sun gaza tsallake gwajin shekarun ‘yan ƙasa da 17

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Lokacin na ƙara ƙurewa tawagar Kamaru ta ’yan qasa da shekara 17 domin bayar da sunayen ’yan wasan da za su buga mata wasannin share fage na Gasar Kofin nahiyar Afrika. Wannan ya biyo bayan matsawar da Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Ƙasar, Samuel Eto’o ya yi, kan cewa sai an yi wa ko wanne ɗan wasa gwaji, wanda da yawa suka gaza tsallake gwajin. Tsohon ɗan wasan Barcelona da Inter Milan ya dage sai an yi amfani da na’urar gwajin shekaru ta (MRI) domin tantance ’yan wasan a filin atisayensu da ke Mbankomo, a wajen…
Read More
Ni ɗan wasa ne na musamman, inji Ronaldo

Ni ɗan wasa ne na musamman, inji Ronaldo

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Cristiano Ronaldo ya bayyana kansa a matsayin ɗan wasa na musamman, sannan ya haƙiƙance cewa, zamaninsa bai ƙare ba a daidai lokacin da ya koma sabuwar ƙungiyarsa ta Al Nassr da ke ƙasar Saudiyya. Ɗan wasan gaban na Portugal mai shekaru 37, ya rattaba hannu kan gagarumar yarjejeniyar da aka kiyasta darajarta kan Yuro miliyan 200 bayan ya kammala zamansa a Manchester United da Real Madrid da Juventus. "Ni ɗan wasa ne na musamman. Na ji daɗin zuwa nan, na kafa dukkanin tarihi a nahiyar Turai, kuma ina son na kafa a Saudiyya,” inji Ronaldo. Ɗan…
Read More
Za mu buƙaci kowace ƙasa ta sanya sunan Pele a filin wasanta – FIFA

Za mu buƙaci kowace ƙasa ta sanya sunan Pele a filin wasanta – FIFA

Daga BASHIR ISAH Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA), ta ce za ta buƙaci ƙasashen duniya kowacce ta sanya wa filin wasannin motsa jikinta sunan gwarzon ɗan ƙwallon ƙafar nan da ya mutu kwannan nan, wato Pele. FIFA za ta buƙaci hakan ne domin ci gaba da raya sunan marigayin wanda ya yi zarra a fagen wasan ƙwallon ƙafa a duniya. Pele, wanda ɗan asalin ƙasar Brazilia ne, ya kwanta dama ne a makon da ya gabata inda ya bar duniya yana da shekara 82. Da yake jawabi a wajen jana'izar marigayin a ranar Litinin, Shugaban FIFA, Gianni Infantino, ya…
Read More
Gobe za a yi jana’izar Pele

Gobe za a yi jana’izar Pele

Daga BASHIR ISAH Gobe Litinin za a yi jana'izar sarkin ƙwallon ƙafa na duniya, wato Pele, wanda ya mutu a ranar Alhamis da ta gabata. Tsohuwar kulob ɗinsa a Brazil, Santos ce ta sanar da hakan a ranar Juma'a. Sanarwar ta ce, "Za a yi jana'izar sarkin ƙwallon ƙafa na duniya a Estadio Urbano Caldeira da ke Vila Belmiro. “Daga Asibitin Albert Einstein za a dauki gwar zuwa babban filin wasa a ranar Litinin." Shugaban Ƙasar Brazil mai barin gado, Jair Bolsonaro, ya ba da hutun kwana uku don zaman makoki game da rasuwar marigayin.
Read More
Cristiano Ronaldo ya koma Saudiyya da wasa

Cristiano Ronaldo ya koma Saudiyya da wasa

Daga WAKILINMU Fitaccen ɗan wasan ƙwallon ƙafar nan, Cristiano Ronaldo ya rattaba hannu kan kwatiragi da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Al-Nassr da ke Saudiyya inda za a biya shi zunzurutun kuɗi miliyan £175 a shekara. Ronaldo ya koma ƙungiyar Al-Nassr ne bayan ficewarsa da ƙungiyar Manchester United watan Nuwamban da ya gabata. Ƙungiyar ta Al Nassr ta tabbatar cewa lallai Ronaldo ya rattaba hannu kan kwangilar shekara biyu da ita. Yanke shawarar komawa Saudiyya ya kawo ƙarshen aikin gwarzon ɗan ƙwallon a matakin farko. Ana tunanin ya daɗe yana fatan ganin ya canza sheka zuwa kulob ɗin gasar Zakarun Turai…
Read More