Daga BASHIR ISAH
Gobe Litinin za a yi jana’izar sarkin ƙwallon ƙafa na duniya, wato Pele, wanda ya mutu a ranar Alhamis da ta gabata.
Tsohuwar kulob ɗinsa a Brazil, Santos ce ta sanar da hakan a ranar Juma’a.
Sanarwar ta ce, “Za a yi jana’izar sarkin ƙwallon ƙafa na duniya a Estadio Urbano Caldeira da ke Vila Belmiro.
“Daga Asibitin Albert Einstein za a dauki gwar zuwa babban filin wasa a ranar Litinin.”
Shugaban Ƙasar Brazil mai barin gado, Jair Bolsonaro, ya ba da hutun kwana uku don zaman makoki game da rasuwar marigayin.