15
Feb
Daga WAKILIN MU Dan wasan damben nan Kamaru Usman, wanda ɗan asalin Nijeriya ne, ya sake lashe kambunsa na UFC bayan da ya doke Gilbert Burns daga ƙasar Brazil a karawar da suka yi a Lahadin da ta gabata. Wannan shi ne karo na uku da Usman ke samun nasarar lashe wannan kambu. Ya samu nasarar farko ne a 2019 bayan da ya doke Colby Covington, sai ta biyu da ya samu a 2020 bayan da ya doke Jorge Masvidal. Yayin wasan baya-bayan nan, Usman bai yi wa Burns da wasa ba inda ya bambance masa tsakanin aya da tsakuwa.…