Wasanni

Messi ya ci wa tawagar Argentina ƙwallo ta 100

Messi ya ci wa tawagar Argentina ƙwallo ta 100

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A daren Talata ne kaftin ɗin Argentina, Lionel Messi ya ci ƙwallonsa ta 100 a wasannin da ya buga na ƙasa da ƙasa, a karawar da ƙasarsa, Argentina ta lallasa Curacao da ci 7 da nema. Messi, wanda sau 7 ya ke lashe kyautar gwani na gwanaye a harkar ƙwallon ƙafar duniya, wadda ake kira Ballon d’Or, shi ya fara saka qwallo a raga a cikin minti na 20 da fara wasan da aka kara a birnin Santiago del Estero. Wannan na zuwa ne shekaru 17 bayan da ya fara ci wa Argentina ƙwallo a wasan…
Read More
Shugaban Man City ya zama mataimakin shugaban Daular Larabawa

Shugaban Man City ya zama mataimakin shugaban Daular Larabawa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta naɗa mamallakin Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Manchester City da ke Ingila, Sheikh Mansour bin Zayed a matsayin sabon Mataimakin Shugaban Ƙasar. A cikin wata sanarwa da Kamfannin Dillancin Labaran ƙasar na Wam ya wallafa, ƙasar ta ce attajirin ya ɗare kujerar ce a matsainsa na shugaban gwamnati. Shugaban Ƙasar ne dai ya sanar da amicewar naɗin, inda ya ce matakin ya biyo bayan amincewar Majalisar Ƙolin Ƙasar na naza Sheikh Mansour a matsayin. Kafin naɗin nasa dai, attajirin shi ne Mataimakin Fira Ministan ƙasar. Bugu da ƙari, Shugaban Ƙasar ya ayyana sunan…
Read More
Mbappe ya zama kaftin ɗin tawagar Faransa

Mbappe ya zama kaftin ɗin tawagar Faransa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Watanni uku bayan shan kayenta a wasan ƙarshe na kofin Duniya, tawagar ƙwallon ƙafar Faransa ta buɗe wani sabon babi a duniyar ƙwallo, inda da dama daga cikin ‘yan wasanta suka yi ritaya, lamarin da ya bai wa Kylian Mbappe damar zama kyaftin ɗin tawagar don tunkarar wasannin neman gurbin shiga gasar cin kofin Turai na EURO 2024. Yayin wasan ƙarshen dai ƙarƙashin gasar kofin Duniya da ta gudana a Ƙatar anga yadda Argentina ta doke Faransa a bugun daga kai sai mai tsaron raga bayan tashi wasa 3 da 3. Babban koma baya ga tawagar…
Read More
Hukumar wasannin guje-guje ta haramta wa mata-maza shiga gasar wasannin mata

Hukumar wasannin guje-guje ta haramta wa mata-maza shiga gasar wasannin mata

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar wasannin guje-guje da tsalle-tsalle ta duniya ta tabbatar da cewa za ta fitar da ’yan wasa mata-maza waɗanda suka sauya halittarsu daga maza zuwa mata daga shiga gasar mata. Shugaban hukumar wasannin guje-guje da tsalle-tsalle na duniya, Lord Coe ya ce, “Mun kuma ɗauki kwakkwaran mataki don kare nau’in mata a wasanninmu, da yin hakan ta hanyar taƙaita shigar ’yan wasa mata-maza. “An hanke shawarar ne tare da tuntuvar masu ruwa da tsaki da dama da suka haɗa da ƙungiyoyin mambobi 40, da ’yan wasanmu, da masu horar da mu da kuma ta hukumar ’yan…
Read More
Yadda jadawalin gasar Europa ya kasance

Yadda jadawalin gasar Europa ya kasance

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An kammala zagayen ’yan 16 na gasar Europa, inda a yanzu ƙungiyoyi 8 suka samu damar tsallakawa zagayen daf da na kusa da na ƙarshe a gasar. Manchester United da Sevilla za su kara a wasan quarter final a gasar zakarun Turai ta Europa League. Ƙungiyoyin da suka kai wannan mataki sun haɗa da Sporting Lisbon da Feyenoord da Juventus da Manchester United da Roma da Sevilla da Union Saint-Gilloise sai kuma Bayer Leverkusen. Arsenal da aka saran za ta taɓuka abin azo a gani a gasar ta bana, ganin irin tagomashin da ta ke samu…
Read More
Yadda jadawalin wasannin daf da na kusa da na ƙarshe na gasar Zakarun Turai ya kasance

Yadda jadawalin wasannin daf da na kusa da na ƙarshe na gasar Zakarun Turai ya kasance

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Juma’a Hukumar Ƙwallon Ƙafar Turai (UEFA) suka fitar da jadawalin matakin ƙungiyoyi takwas ɗin ƙarshe na Gasar Zakarun Turai. A ƙunshin jadawalin, Real Madrid za ta fafata da Chelsea a matakin daf da na kusa da na ƙarshe a babbar gasar Turan ta bana. Ko a kakar da ta gabata, ƙungiyoyin sun haɗu a irin wannan matakin inda Real Madrid ta samu nasara a kan Chelsea. A bana dai Real ta kawo wannan matakin, bayan da ta fitar da Liverpool da cin 6-2 gida da waje a kakar bana. Ita kuwa Chelsea ta yi…
Read More
Bayern Munich ta daƙile burin PSG na lashe gasar Zakarun Turai

Bayern Munich ta daƙile burin PSG na lashe gasar Zakarun Turai

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Bayern Munich ta kawo ƙarshen fatan PSG na lashe kofin zakarun Turai cikin wannan kaka, bayan da ta lallasata da ƙwallaye biyu da nema a wasansu na daren ranar Laraba. Tun a haɗuwar farko dama Bayern Munich ta lallasa PSG da ƙwallo 1 mai ban haushi har gidanta cikin watan jiya, gabanin nasarar ta daren ranar wanda ke nuna tauraruwar ta Jamus ta doke zakarar ta Faransa da ƙwallaye 3 da nema a jumlace. Cikin shekaru 11 da PSG ta shafe ta na fafutukar ganin ta lashe kofin na zakarun Turai, wannan…
Read More
Chelsea ta kai zagayen daf da kusa da ƙarshe a gasar Zakarun Turai

Chelsea ta kai zagayen daf da kusa da ƙarshe a gasar Zakarun Turai

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Chelsea ta farfaɗo da fatanta a kakar wasan bana, bayan da ta doke Borussia Dortmud da ci 2 da nema a karawar da suka yi a Stamford Bridge, inda a yanzu ta kai zagayen daf da na kusa da na ƙarshe a gasar zakarun Turai. Raheem Sterling ne ya fara jefawa Chelsea ƙwallo kafin Kai Havertz ya jefa ta biyo a bugun daga kai sai mai tsaron gida. Mai horar da ƙungiyar Graham Potter na fuskantar matsin lamba bayan da kwalliya ta gaza biyan kuɗin sabulu, ganin yadda ƙungiyar ta kafa tarihin…
Read More
Liverpool ta yi wa Manchester united wankan jego

Liverpool ta yi wa Manchester united wankan jego

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Liverpool ta yi wa Manchester United aiki mai sauƙi inda ta lallasa ta da ci 7 rigis a wasan Gasar Premier a yammacin Lahadi. Tauraron ɗan ƙwallon Netherlands Cody Gakpo, Mohamed Salah, da Darwin Nunez sun nuna bajinta matuƙa a filin wasa na Anfield, inda suka zura ƙwallaye biyu kowannensu a ragar abokan hamayyarsu ta Manchester. Tawagar ta Jurgen Klopp dai sun kafa sabon tarihin nasara a fafatawar da aka yi tsakanin ƙungiyoyin biyu da suka fi samun nasara a gasar Ingila. Kawo yanzu dai Mohamed Salah ya zama kan gaba…
Read More
Arsenal ta lallasa Everton karo na 100 a tarihi

Arsenal ta lallasa Everton karo na 100 a tarihi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Arsenal ta ci Everton 4-0 a kwatan wasan Firimiya da suka kara ranar Laraba a Emirates. Wasa ne da ya kamata su fafata tun ranar 11 ga watan Satumbar 2022. Arsenal ta ci qwallo ta hannun Bukayo Saka saura minti biyar su yi hutu, sannan Gabriel Martinelli ya ƙara na biyu daf da cikar minti na 45. Kyaftin ɗin Arsenal, Martin Odegaard shine ya ƙara na biyu, saura minti 19 a tashi daga karawar daga baya Martinelli ya aara na biyu na huɗu a wasan. Wannan shine karo na 100 da Arsenal ta ci Everton a…
Read More