Wasanni

Yadda Real Madrid ta fitar da Man City daga gasar Zakarun Turai

Yadda Real Madrid ta fitar da Man City daga gasar Zakarun Turai

Real Madrid ta fitar da Manchester City a wasan cike gurbi a Gasar Zakarun Turai, bayan da ta ci 3-1 ranar Laraba a Santiago Bernabeu. Real Madrid ta kai zagayen gaba da cin 6-3 gida da waje kenan, bayan da ta yi nasara 3-2 a Etihad ranar Talata 11 ga watan Fabrairu. City ta ci ƙwallo biyu ta hannun Erling Haaland a Etihad, yayin da Kylian Mbappe da Brahim Diaz da Jude Bellingham suka ci wa Real Madrid ƙwallayenta. Kylian Mbappe ne ya fara cin ƙwallo a minti na 4 da fara wasan, karon farko da Real ta ci ƙwallo…
Read More
Lookman ya bayyana takaici kan kalaman kocinsa

Lookman ya bayyana takaici kan kalaman kocinsa

Ademola Lookman ya ce, ya ji takaicin irin kalaman da kocinsa Gian Piero Gasperini ya yi a kansa, bayan da ya kwatanta ɗan wasan da "wanda ya fi kowa rashin iya buga fenareti" da ya taɓa gani. Kocin ya yi kalaman ne bayan da Atalanta ta yi rashin nasara a hannun Club Brugge da ci 3-1 ranar Talata a gasar Zakarun Turai, abu kuma da ya sa ƙungiyar ta fice daga gasar da ƙwallo 5-1 gida da waje. "Abin ɓacin rai ne in yi martani a irin wannan rana, saboda abin da muka cimma a matsayin ƙungiya," kamar yadda Lookman…
Read More
Man United za ta ƙara rage ma’aikata

Man United za ta ƙara rage ma’aikata

Daya daga wanda ya yi haɗakar mallakar Manchester United, Sir Jim Ratcliffe na duba yiwuyar yadda za a ƙara rage ma'aikatan ƙungiyar. Wata majiya ta tabbar da cewar Man United na duba yadda za ta kara rage kuɗin da take kashewa da zai kai yuro miliyan 300 a shekara uku. Man United ba ta ce komai ba kan rahoton cewar Ineos Group, ƙarƙashin Ratcliffe na auna yadda zai sake rage ma'aikata kimanin 100 zuwa 200 ba. Daga baya ne za a fayyace yawan ma'aikatan da za a rage da guraben da suke aiki, domin aiwatar da shirin. Haka kuma United…
Read More
Shahararrun ’yan wasa da asalinsu ‘yan Nijeriya ne amma suke wakiltar wasu ƙasashe

Shahararrun ’yan wasa da asalinsu ‘yan Nijeriya ne amma suke wakiltar wasu ƙasashe

Akwai wasu zaratan 'yan ƙwallo da asalinsu 'yan Nijeriya ne, amma suke wakiltar wasu ƙasashen duniya. Wasu zaratan 'yan ƙwallo da tauraronsu ke haskawa a duniya, waɗanda asalin 'yan Nijeriya ne, wato ko dai iyayensu bakiɗaya ko wani ɓangare daga cikin iyayen nasu ’yan Nijeriya ne. Na farko shi ne - Jamal Musiala: Jamal Musiala, wanda aka haifa a ranar 26 ga Fabrairun shekarar 2003, fitaccen ɗan ƙwallon ƙasar Jamus ne da ƙungiyar Bayern Munich ta Jamus ɗin kuma yana cikin matasan 'yan ƙwallon da suke tashe a duniya a yanzu. An haife shi ne a garin Stuttgart da ke…
Read More
Kano Pillars ta dakatar da kocinta, Usman Abdallah

Kano Pillars ta dakatar da kocinta, Usman Abdallah

Hukumar Gudanarwar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ta dakatar da mai horar da 'yan wasanta, Usman Abdallah har tsawon makonni uku. Sanarwar da shugaban hukumar gudanarwar ƙungiyar, Alhaji Ali Muhammad Umar ya fitar, ta ce mataimakin mao horarwar, Ahamd Garba Yaro-Yaro ne zai ci gaba da riƙon muƙamin nasa. Wannan ya biyo bayan rashin kataɓus ɗin da ƙungiyar ta yi a baya-bayan nan, haɗi da harzuƙa magoya bayan ƙungiyar, bayan tashi daga wasan da Kano Pillars din ta yi kunnen doki da Bayelsa United a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano. Sanarwar ta ci gaba da cewa,…
Read More
Barcelona ce kan gaba wajen zura ƙwallaye a La Liga

Barcelona ce kan gaba wajen zura ƙwallaye a La Liga

Kungiyar Barcelona ce kan gaba a yawan zura ƙwallaye a raga a kakar nan mai 59 kawo yanzu, bayan da aka kammala wasannin sati na 21 a ƙarshen mako. A ranar Lahadi Barcelona ta caskara Valencia da cin 7-1 a babbar gasar tamaula ta Sifaniya da suka kara. Waɗanda suka ci wa Barcelona ƙwallayen sun haɗa da Frenkie de Jong da Ferran Torres da Raphinha da Fermin Lopez da ya ci biyu da Robert Lewandowski da kuma Cesar Tarrega da ya ci gida. Sai dai Valencia ta zare ɗaya ta hannun Hugo Duro, bayan da suka yi hutu suka koma…
Read More
Neymar ya soke kwantiraginsa da Al-Hilal ta Saudiyya

Neymar ya soke kwantiraginsa da Al-Hilal ta Saudiyya

Kungiyar Al-Hilal ta Saudiyya da ɗan wasan Brazil Neymar sun amince su kawo ƙarshen kwantaragin ɗan wasan. Neymar, mai shekara 32 a duniya ɗan asalin ƙasar Brazil ya je Al-Hilal ne a watan Agustan shekarar 2023 kan kuɗi Yuro miliyan 90, sai dai sau bakwai kacal ya buga wa ƙungiyar wasa sanadiyyar rauni da ya addabe shi. A kakar da ke ci sau biyu kawai Neymar ya buga wasa, na baya-bayan shi ne lokacin da aka yi canji da shi a watan Nuwamba. Ana alaƙanta shi da komawa ƙungiyarsa ta asali, wato Santos, da ke Brazil. "Kungiyar ta gode wa…
Read More
An kama ɗan wasan Belgium, Nainggolan bisa zargin safarar hodar iblis

An kama ɗan wasan Belgium, Nainggolan bisa zargin safarar hodar iblis

An kama ɗan wasan ƙwallon ƙafar ƙasar Belgium Radja Nainggolan a wani ɓangare na bincike kan safarar hodar iblis. Dan wasan mai shekaru 36, yana ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin ’yan sandan Belgium ne suka kama a safiyar ranar Litinin, bayan wasu samame daban-daban da aka kai a faɗin ƙasar. "Binciken ya shafi bayanan da ake zargin an shigo da hodar iblis daga Kudancin Amurka zuwa Turai, ta tashar ruwa ta Antwerp, da kuma sake rarraba shi a Belgium," inji ofishin mai gabatar da ƙara na Brussels a cikin wata sanarwa. Babu wani ƙarin bayani da aka bayar ga…
Read More
Matsalolin Man United ba sa ruɗani – Amorim

Matsalolin Man United ba sa ruɗani – Amorim

Ruben Amorim ya yi amai ya lashe kan kalaman da ya yi cewar ƙungiyarsa ta Manchester United ta kakar nan ita ce mafi muni a tarihi. Sai dai ya ce ba zai yi yaudara ba da cewar ba su da manyan matsaloli ba a kasa. Amorim ya ce ya yi kuskure da ya samar da baraka lokacin da ya fuskanci ’yan wasa nan take, bayan tashi karawar da Brighton ta yi nasara 3-1 a Premier League. Hakan ya sa ya gana da ’yan jarida cikin fushi da ta kai ya faɗi wasu kalaman. An tambaye shi ko ya san cece-kucen…
Read More
AFCON 2025: Super Eagles za su san abokan karawarsu a Rabat

AFCON 2025: Super Eagles za su san abokan karawarsu a Rabat

Gabanin fitar da jadawalin gasar kofin nahiyar Afirka na shekarar 2025, Super Eagles ta Nijeriya za ta gano abokan karawarta a rukuni a Rabat, babban birnin ƙasar Moroko. Hukumar Kula da ƙwallon ƙafa ta Afirka (CAF) ta sanar a ranar Talata cewa Rabat ce za ta karvi baƙuncin gasar. Gasar dai za ta ƙunshi ƙungiyoyi shida ne, kowanne da ƙungiyoyi huɗu. ƙungiyoyin biyu na farko daga kowane rukuni, tare da ƙungiyoyi huɗu mafi kyau a matsayi na uku, za su wuce zuwa zagaye na 16. Tare da fafatawar, ƙasashen da ke halartar gasar za su kuma sami damar tantance wuraren…
Read More