CHAN 2025: Super Eagles ta gayyaci ’yan wasan Kano Pillars uku

Spread the love

Kocin Super Eagles, Austin Eguavon ya gayyaci ’yan Kano Pillars uku ciki har da Rabi’u Ali, domin karawa da Ghana a neman shiga gasar CHAN 2025.

Sauran da aka kira daga Pillars sun haɗa da Abiam Nelson da kuma Adams Aminu Sani a tawagar ta Super Eagles masu taka leda a gida.

Rabi’u Ali yana kan ganiya a wasannin firimiyar Nijeriya ta bana, wanda ya zura ƙwallo takwas a raga, bayan kammala wasannin mako na 15.

Ana sa ran ’yan wasan da aka gayyata za su je katafaren filin wasa na Remo Stars a Ikenne da ke jihar Ogun daga ranar 4 ga watan Disamba, domin karɓar horo.

Super Eagles za ta fara zuwa Ghana a wasan farko ranar 22 ga watan Disamba, sannan a buga fafatawa ta biyu ranar 28 ga watan Disamba a Godswill Akpabio Stadium a Uyo jihar Akwa Ibom.

Za a buga gasar CHAN 2025 ta ’yan wasan da ke taka leda a gida a cikin watan Fabrairun 2025 a Kenya da Uganda da kuma Tanzania.

Ghana ta yi wa Super Eagles fintinkau a zuwa gasar CHAN a 2009 da kuma 2023, inda Nijeriya ta zama ’yar kallo.

By ukarofi