
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun 25 da 26 ga watan Disambar 2025 da kuma 1 ga watan Junairun 2026 a matsayin lokacin hutun bikin Kirsimeti, ranar boksin da kuma murnar shiga sabuwar shekara.
Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Dakta Magdalene Ajani ta bayyana haka a wata takarda, yau Litinin.
Ta ce, Ministan ma’aikatar, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo ya sanar da haka a madadin Gwamnatin Tarayyar.
Ya yi kira ga al’umma da su yi amfani da lokacin wajen ƙarfafa soyayya, zaman lafiya, tausayi da sadaukarwa a tsakaninsu yayin tunawa da zagayowar ranar haihuwar Annabi Isa (AS).
Tunji-Ojo ya kuma kirayi ƴan Nijeriya daga kowane addini ko ƙabila da su yi amfani da lokacin wajen yi wa ƙasar addu’o’in samun zaman lafiya, tsaro da ci-gaba.
Haka kuma, ministan ya roƙi ƴan ƙasa da su cigaba da kasancewa masu ƙoƙarin kiyaye doka da oda da sanya ido akan lamuran da suka shafi tsaro a yayin bukukuwan.
