Daga BASHIR ISAH
Shugaba Bola Tinubu ya yi kira ga ‘yan kasuwa na ƙasa da ƙasa kan cewa kada su bai kowa cin hanci kafin gudanar da harkokinsu a Nijeriya, kuma duk wani jami’insa da ya nemi a ba shi cin hancin a kai ƙararsa.
Tinubu ya bayyana haka ne sa’ilin da yake jawabi a wajen taron Zuba Jarida na Nigeria-Qatar ranar Lahadi a Doha, Qatar.
A cewarsa, “Kada ku bai wa kowa cin hanci, kuma duk wanda ya karɓa ko ya nemi ku ba shi cin hanci, ku sanar da mu.”
Shugaban ya ƙara da cewa a shirye Nijeriya take don yin kasuwanci, kuma gwamnatinsa za ta ɗauki mataki a kan duk wanda ya yi ƙoƙarin cire wa masu zuba jari a ƙasar ƙwaron gwiwa.
Tinubu ya yi alƙawarin kawar da duk wani abu da zai haifar da cikas ga samun riba ga ‘yan kasuwar da suka yi nufin zuba jari a Nijeriya.
Ya shaida wa taron an bunƙasa tsare-tsaren tattalin arzikin Nijeriya wadda ta kasance ƙasa mafi ƙarfin tattalin arziki a nahiyar Afirka.
Kazalika, Shugaban ya bai wa ‘yan kasuwar tabbacin samun zarafin ta’ammali da ofishin Shugaban Ƙasa ba tare da wata wahala ba a duk lokacin da buƙatar hakan ta taso.
Ta bakinsa a wajen taron, “Na zo nan ne don ba ku tabbacin ingantattun sauye-sauyen da ke gudana a fannin tattalin arzikin Nijeriya, ku mance da duk abin da kuka ji a baya.
“Duk wata matsala ko cikas da wasunku suka fuskanta, wannan a baya ne, domin babu irin wannan matsala a gaba,” in ji shi.
