Yadda aka yi wa ’yan canji rusau a Abuja

Spread the love

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja

Hukumar Babban Birnin Tarayya ta yi rusau a babbar cibiyar hada-hadar ’yan canji da ke Unguwar Zone 4 da ke Abuja.

An rusa rumfunan wucin gadi da bacoci tare da sare bishiyoyi a yayin aikin rusau ɗin da aka gudanar ranar Laraba.

Daraktan Sashen Kula da Gine-gine na hukumar, Mukhtar Galadima, wanda ya jagoranci aikin, ya bayyana wa ’yan jarida cewa ɓata-gari suna amfani bacocin da rumfunan wucin gadin da ke wurin a matsayin maɓoyarsu a birnin.

Mukhtar Galadima ya ƙara da cewa wurin ya zama cibiyar masu aikata manyan laifuka, wanda hakan barazana ce don haka ya zama dole a kawar da ita.

A cewarsa, lura da yadda wurin ya zama abin ƙyamar, matakin da aka ɗauka zai ƙara fito da kyawun birnin na Abuja.

Ya ƙara da cewa, ya zama wajibi ga ’yan canji su riƙa gudanar da harkokinsu a wuraren da aka ware musu ba a ƙarƙashin bishiyoyi ba ko a cikin daji kamar yadda ake yi a Zone 4.

Amma ya ce aikin nasu ba shi da alaqa da neman musguna wa ’yan canji, illa kawai neman tabbatar da tsafta da kuma tsaron lafiya da dukiyoyin jama’a.

Da aka tambaye shi dalilin rashin gina filin da suka yi rusau ɗin, sai ya ce ana shari’a ne a kan filin, ana jira ne kotu ta yanke hukunci.

“Amma duk da haka tsaron rayuka na da muhimmanci, shi ya sa dole muka ɗauki wannan mataki,” inji shi.

By Editor