Gwamnatin Kano ta karɓi tawagar ‘Lives and Livelihood Foundation’ don haɗin gwiwa a fannin lafiya da noma  

Spread the love

Daga RABIU SANUSI a Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karɓi tawagar Lives and Livelihood Foundation, wacce ta kai ziyarar ban girma ga Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf a Fadar Gwamnati, domin tattauna hanyoyin haɓaka haɗin gwiwa a fannonin lafiya da noma.

Da yake jawabi yayin ziyarar, shugaban tawagar gidauniyar, Ali Ahmad Al-Gandi, ya bayyana cewa gidauniyar tana da cikakken ƙuduri na inganta walwalar al’umma ta hanyar ƙarfafa kula da lafiya a matakin farko, rigakafin cututtuka, da kuma tallafawa manoma a faɗin jihar.

Al-Gandi ya ce Jihar Kano tana daga cikin muhimman abokan hulɗar gidauniyar, la’akari da yawan jama’arta da kuma tsare-tsaren ci gaba da gwamnatin Abba Kabir Yusuf ke aiwatarwa a fannoni na zamantakewa da tattalin arziki.

A jawabinsa madadin Gwamna, Babban Sakataren Gwamnati, Dr. Sulaiman Wali (mni), ya tarbi tawagar tare da jinjinawa gidauniyar bisa jajircewarta wajen tallafawa shirye-shiryen ci gaban jihar. Ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta kuduri aniyar faɗaɗa damar samun ingantattun ayyukan lafiya da bunƙasa harkar noma, musamman a tsakanin al’ummomin karkara da ƙananan manoma, domin samar da dorewar ci gaban tattalin arziki.

Tun da farko, Kwamishinan Lafiya, Alhaji Abubakar Labaran Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatin jihar a buɗe take ga duk wata haɗin gwiwa da ta yi daidai da manufofinta na raya al’umma. Ya tabbatar da shirin gwamnatin jihar na yin aiki kafaɗa da kafaɗa da gidauniyar wajen aiwatar da shirye-shiryen da za su haifar da ayyukan yi, rage talauci, da inganta jin daɗin jama’a.

Taron ya ƙare da cimma matsaya kan kafa ƙungiyar haɗin gwiwa ta fasaha domin tsara da daidaita muhimman fannoni na haɗin kai, musamman wajen ƙarfafa tsarin kula da lafiya a matakin farko da bunƙasa noman zamani mai ɗorewa a faɗin jihar.

By ukarofi