Janairun baɗi za a fara bai wa ɗalibai bashi a Nijeriya – Tinubu

Spread the love

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa, ya zuwa watan Janairun 2024 shirinsa na bai wa ɗalibai bashi zai kankama.

Ya bayyana haka ne sa’ilin da yake jawabi a wajen taron tattalin arziki na ƙasa na 2023 ranar Litinin a Abuja.

“Ya zuwa Janairun 2024, sabon shirin bai wa ɗalibai bashi zai fara aiki. Don haka muke cewa babu sauran tafiya yajin aiki a rayuwar ‘ya’yanmu kuma ɗalibai a nan gaba,” in ji Tinubu.

A ranar bikin “June 12” Shugaba Tinubu ya sanya wa ƙudirin bai wa ɗalibai bashi hannu ya zama doka, alƙawarin da ya ɗauka a lokacin yaƙin neman zaɓensa.

Kakakin Majalisa Wakilai a majalisa ta 9 kuma Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa a yanzu, Femi Gbajabiamila ne ya gabatar da ƙudirin domin bai wa ‘yan ƙasa samu zarafi zurfafa karatu cikin sauƙi.

By Editor