Kaduna: ‘Yan sanda sun zayyano ‘yan cocin Kajuru da aka sace bayan ƙaryata harin da fari

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Rundunar ‘yan sanda ta tabbatar da rahotannin cewa ‘yan bindiga sun yi awon-gaba da mutane da dama na ƙauyen Kurmin Wali da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru a jihar Kaduna bayan da fari reshen rundunar na Kaduna ya ƙaryata.

A wata sanarwa da ta fitar a yammacin ranar Talata daga jami’in hulɗa da jama’arta, ACP Olumuyiwa Adejobi ta Kakakin rundunar, Benjamin Hundeyin, rundunar ta ce harin ya auku ne a ranar Lahadi, inda ta ce tuni aka tura jami’ai domin ƙaddamar da atisayen ceto waɗanda al’amarin ya shafa.

Ya bayyana cewa, da fari ‘yan sanda da gwamnatin Kaduna sun musanta rahotannin ne domin kauce wa haddasa firgici acikin al’umma yayin da ake ƙoƙarin tabbatar da rahoton, zancen da ƙungiyoyin al’umma da na jagororin addini suka riƙa suka.

Duk da cewa rundunar ba ta bayyana haƙiƙanin adadin waɗanda aka sace ba, majiyoyi da dama sun ce harin na ɗaya daga cikin mafi girma da aka kai a ‘yan watannin nan.

Wani ɗan majalisar Kaduna mai suna Usman Ɗanlami Stingo ya shaida wa manema labarai cewa aƙalla mutanen da aka yi garkuwar da su za su kai 168 yayin ƙungiyar Kiristocin Nijeriya (CAN) a Arewa ta ce aƙalla masu ibada 172 ne aka sace waɗanda daga ciki guda tara suka tsere.

A cewar shaidu da rahoton ‘yan sanda, al’amarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:25 na ranar Lahadi a lokacin da mutanen suke tsaka da ibada a Cocin ECWA da cocinan Cherubim da Seraphim na 1 da 2 a Kurmin Wali.

Rahoton ya bayyana cewa, ‘yan bindigar sun je yankin ne ɗauke da wasu muggan makamai,wanda hakan ya sanya mutane da dama tserewa zuwa dazukan da ke kewayen yankin. A yayin haka ne suka yi nasarar awon-gaba da masu yawa daga cikinsu.

Ga jaddawalin waɗanda aka sacen kamar yadda masu sharhi suka bayyana na wasu daga cikin iyalai shida:

Jonathan – mutane 12

Amos – 13 mutane

Markus/Makudi – 10

Ishaya da Danisa – 7 ga kowannensu

Bawa – mutane 6

Danjuma da Musa – 5 ga kowane gida.

Sauran sun haɗa da:

  1. Zahaya Joshua
  2. Nabilah Makudi
  3. Hajara Makudi
  4. Rebecca Hosea
  5. Ahmad Ahmad
  6. Liyu Ezekiel
  7. Vivian Ezekiel
  8. Goodluck Ezekiel
  9. Beauty Ezekiel
  10. Matina Maiyashi
  11. Bridget Maiyashi
  12. Vivian Linus
  13. Mary Amos
  14. Hamid Amos
  15. Patricia Amos
  16. Hamisu Amos
  17. Luka Amos
  18. Tacy Amos
  19. Cynthia Amos (guessed)
  20. Mercy Isaac
  21. Augustine Makudi
  22. Matthew Samaila
  23. Adam Musa
  24. Malika Sule
  25. Abu Ahmad
  26. Hussein Lucky (guessed)
  27. Akinyi Sadiu
  28. Dangata Amos
  29. Helen Jonathan
  30. Asinwa Jonathan
  31. Faith Joseph
  32. Gloria Kennet
  33. Happiness Danisa
  34. Fidelis Jacob
  35. Tobias Markus
  36. Istu Paul
  37. Hassana Paul
  38. Charity Chindo
  39. Christiana Danisa
  40. Everest Danima
  41. Thomas Philip
  42. Catrina Danbosi
  43. Halima Hassan
  44. Hassan Lukumi
  45. Mary Sadiu
  46. Franca John
  47. Henry Danbiyi
  48. Genesis Lawal
  49. Ayuba Lawal
  50. Solomon Ayuba
  51. Theophilus Danlami (guessed)
  52. Charles Sambo
  53. Rahila Charles
  54. Gambo Danisa
  55. Talent Danisa
  56. Nehemiah Danjuma
  57. Maijima Shekarau
  58. Matina Maijima
  59. Laraba Maijima
  60. Musa Danjuma
  61. Ishaya Danima
  62. Lulu Danisa
  63. Clement Ahmad
  64. Destiny Ahmad
  65. Nehemiah Ishaya
  66. Simon Ishaya
  67. Nasty Muku
  68. Helena Joseph
  69. Joseph Bawa
  70. Sarah Joseph
  71. Bulus Mariya
  72. Musa Samaila
  73. Bulus Bawa
  74. Halima Bawa
  75. Beture Hosea
  76. Sati Hosea
  77. Titus John
  78. Dogara Bawa
  79. Lories Bawa
  80. Adamu Aminu
  81. Ezekiel Adamu
  82. Tenah Markus
  83. Patricio Bawa
  84. Janet Tsuda
  85. Amina Danjuma
  86. Sandra Danbosi
  87. Bridget Sunday
  88. Saphat Innocent (baƙuwa)
  89. Alex Sunday
  90. Beauty Peter
  91. Samisa Paul
  92. Joy Joseph
  93. Methole Johanna
  94. Genesis Johanna
  95. Maria Johanna
  96. Merozdu Adonu
  97. Karimi Jangbe
  98. Sunday Martela
  99. Santina Hershinga
  100. Keuna Michael
  101. Hassan Bulus
  102. Marzeta Maisoni
  103. Mainwa Dominic
  104. Godwin Karimi
  105. Amos Akijo
  106. Nathan Amos
  107. Joseph Chindo
  108. Lydia Godwin
  109. Hamna Maiyangi
  110. Toletu Maiyangi
  111. Esther Godday
  112. Godlive Samson
  113. Goodluck Aliga
  114. Madaki Tabawa
  115. Tabawa Abba
  116. Tabawa Iyamye
  117. Samuel Amos
  118. Daniel Amos
  119. Deborah Amos
  120. Ruth Amos
  121. Emmanuel Danjuma
  122. Joshua Danjuma
  123. Rejoice Danisa
  124. Blessing Danisa
  125. Ibrahim Lawal
  126. Zainab Lawal
  127. Sadiq Ahmad
  128. Aisha Ahmad
  129. Yakubu Musa
  130. Suleiman Musa
  131. Rahama Musa
  132. Daniel Jonathan
  133. Samuel Jonathan
  134. Peter Jonathan
  135. Grace Jonathan.

Tuni dai rundunar ‘yan sandan Kaduna ta ce ta fara gudanar da binciken akan al’amarin domin ganin an ceto mutanen cikin aminci.

By Babaji