Daga BASHIR ISAH
Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN) ta nada Mataimakin Shugaba na Shuyyar Arewa ta Tsaki, Malam Habibu Barde, a matsayin shugaban riko na kasa na kungiya.
Sanarwar nadin na kunshe ne cikin sanarwar manema labaran da Kwamitin Amintattu na kungiyar ya fitar a ranar Laraba mai dauke da sa hannun shugabansa, Makama Sani Mu’azu.
Sanarwar ta kuma nuna cewa nadin Barde a matsayin Shugaban riko na kungiyar ya fara aiki ne nan take.
A cewar danarwar, “Nadin ya biyo bayan ajiye mukaminsa da Dr. Ahmad Sarari ya yi ne a matsayin Shugaban Kungiyar.”
Keamitin ya nuna godiyarsa ga Dr Ahmad Sarari bisa dawainiyar da ya yi da kungiyar wajen ciyar da ita gaba a tsakanin shekarun da ya shafe rike da ita.
MOPPAN na daga cikin fitattun kungiyar masu shirya finafinai a Nijeriya mai mamabobi da dama da kuma rassa a fadin kasa.