Nijeriya za ta yi aiki da Pakistan wajen maganin masu tada zaune tsaye – Magashi

Spread the love

Daga BASHIR ISAH

Ministan Tsaro, Manjo Janar Bashir Salihi Magashi (mai murabus) ya sha alwashin Nijeriya za ta ci gaba da yin aiki tare da sojijin Pakistan a matsayin wani ƙoƙari na kawo ƙarshen fitinar masu tsattsaurar ra’ayi.

Janar Magashi ya bayyana haka ne sa’ilin da babban jami’in sojan Pakistan, Janar Nadeem Raza ya ziyarce shi a Hedikwatar Tsaro da ke Abuja a Juma’ar da ta gabata.

Magashi ya ce Nijeriya da Pakistan na da manufa iri guda ta fuskar neman daƙile harkokin masu tada ƙayar baya a cikin ƙasa.

Ministan wanda ya samu horo a wani ɓangaren aikinsa a ƙasar Pakistan ya ce duba da yadda ‘yan ta’adda a sassan duniya kan haɗa kai wajen aiwatar da harkokinsu da kuma barazana ga lumanar al’umma, akwaii buƙatar a yi aikin haɗin gwiwa tsakanin ƙashe don yi wa miyagun taron dangi.

Cikin wata sanarwar da da hadimin ministan, Mohammed Abduƙadir ya fitar, ministan ya ba da tabbacin cewa a shirye Nijeriya take ta tatsa daga hikimar da Pakistan ke da ita wajen magance matsalolin tsaro.

A nasa ɓangaren, Janar Nadeem Raza ya yi godiya da irin tarbar da ya samu a wajen ministan wanda a cewarsa hakan ya buɗe wani sabon shafi don sojojin ƙasashen biyu su yi aiki tare.

By Editor