Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya bai wa ‘yan Nijeriya tabbaci kan su sa ran samun walwala nan ba da dadewa ba.
Tabbacin Shugaban na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da kokawa kan tsadar rayuwar da suke fuskanta wadda cire tallafin mai ya haifar.
Tinubu ya ba da tabbacin haka ne a sakon Kirsimetin da ya aike wa ‘yan kasa, musamman mabiya addinin Kirista, albarkacin bikin Kirsimetin da al’ummar Kirista ke gudanarwa a wannan Litinin a duk fadin duniya.
Shuagaban ya ce gwamnatinsa ta bada himma ainun wajen aiwatar da ingantattun matakan da za su taimaka wajen rage wa ‘yan kasa radadin rayuwar da suke fuskanta.