Daga WAKILINMU
Hukumar tsaro ta DSS ta sanar cewa ta cafke wanda ake zargi ya jagoranci dana bom din da ya tashi a yayin da Shugaba Buhari ke ziyarar aiki a Jihar Kogi.
A ranar 29 ga Disamba, 2022 ne bom ya tashi kusa da Fadar Sarki Ohinoyi na Kasar Ibira a Okene, Jihar Kogi yayin da Shugaba Buhari ke ziyarar aiki a masarautar.
Mai magana da yawun DSS, Peter Afunanya, ya faɗa a ranar Laraba cewa, “Yayin bincikensu an gano wanda aka cafken babban kwamanda ne a ISWAP.
“Ya jagoranci ko yana da hannu a hare-haren da aka kai ofishin ’yan sanda a Karamar Hukumar Okehi, Jihar Kogi a 2022 inda jami’i daya ya rasa ransa.
“Shi ne kuma ya kitsa Harin Gidan Yarin Kuje a Abuja a watan Yuli da kuma harin da aka kai kamfanin WACL a Ajaokuta duk a shekarar 2022.
“Ana kuma zargin sa da hannu a harkar satar mutane a jihohin Kogi da Ondo,” in ji jami’in.
Afunanya ya ce ana tsare da wanda ake zargin tare da wanda ta kama su tare, kuma za a gurfanar da su a kotu nan gaba kadan.
Ya jadadda cewa hukumar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ci gaba da kare rayuka da dukiyar al’uma kamar yadda ya rataya a kanta.
Aminiya ta rawaito Nna’urar BVAS da ta tattara sakamakon zabe (IReV), na’urori ne wadanda INEC ta shirya yin amfani da su a zabe mai zuwa don gudanar da sahihin zabe.
Okoye ya yaba wa daukacin ‘yan kasa bisa goyon bayan da suke nuna wa hukumar don tabbatar da ta shirya zabe mai tsafta.
