Daga MAHDI M. MUHAMMAD
Rundunar Haɗin Gwiwa ta Operation Delta Safe a yankin Neja Delta ta ce yawan ɗanyen man da ake fitarwa a kowace rana ya kai ganga miliyan 1.7.
Bugu da ƙari, ta ce kamfanonin mai na ƙasa da ƙasa suna aiki a iyakar iya aiki tare da dukkanin manyan bututun mai guda uku suna samun hanyoyi 100.
Kodinetan cibiyar OPDS Joint Media, Manjo Kayode Owolabi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Fatakwal a ranar Lahadin da ta gabata kuma ya aikewa manema labarai.
Owalabi ya ce, a ranar 17 ga watan Yuli, 2024, Babban Hafsan Tsaron ƙasa, Janar Christopher Musa, ya bayar da umarnin kawo ƙarshen satar ɗanyen mai a yankin Neja Delta.
Ya ce, bin umarnin da ke sama, Kwamandan rundunar haɗin gwiwa ta Kudu maso Kudu, Operation Delta Safe, Rear Admiral J. John Okeke, nan take a ranar 18 ga Yuli, 2024, ya fara aiki.
Wasu daga cikin ayyukan bisa ga bayanan sun haɗa da, “jerin ziyartan wayar da kan jama’a, kimanta wuraren da aka kai hari da kuma lalata matatun mai ba bisa ƙa’ida ba, kama kayan satar mai da jiragen ruwan da ke cikin waɗannan ayyukan.
