Za mu gina Nijeriya kamar yadda muka gina Lagos da Borno – Shettima

Daga IBRAHEEM HAMZA MUHAMMAD

Sanata Kashim Shettima ya jaddada cewa, Najeriya za ta mori romon mulkin dimukraɗiyya idan aka zavi Asiwaju Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC a matsayin Shugaban Ƙasa a zaven da ke gabatowa.

A takardar sanarwa da Kakakin Kwamitin APC mai neman a zaɓi Bola Ahmed Tinubu da Sanata Kashim Shettima a matsayin Shugaba da Mataimaki, Mista Bayo Onanuga, ya fitar, ta ce, sanatan ya furta haka ne a ranar Litinin a Legas yayin da ya wakilci Tinubu a taron shekara-shekara na Ƙungiyar Lauyoyi ta Ƙasa (NBA). Inda ya ce, aikin gani-da-ido da Tinubu da Shettima suka aiwatar a Lagos da Borno ya zama manuniyar cewa su masu aiki tuƙuru ne.

Tsohon Gwamnan na Borno ya ce, duk da yanayin rashin tsaro a Arewa Maso Yamma yayin da yake mulki, ya taka rawar gani a fannin ilmi.

Sanata Shettima ya ƙara da cewa, “jama’a suna da alhakin su yaba wa mai aiki a maimakon mai yawan dogon Turanci.

“Ya dace jama’a su bi wanda ya san hanyar zuwa ga ɗaukaka, domin in an zaɓe mu, a ranar farko za mu fara aikin yalwata tattalin arzikin ƙasa, samar da yanayi mai alfanu da kuma inganta tsaro.

“Da Tinubu da ni gwaraza ne da muke son gina ƙasa: Alal misali, ana iya zuwa Jihar Borno, don gani-da-ido kan yadda na gina makarantu, sannan kuma na inganta samar da ilmi gadan-gadan duk da ana yaki da masu ɗauke da makamai a lokacin.

“Ba za mu yi ƙasa a gwuiwa ba wajen kambana ayyukan da muka yi a jihohinmu, don ciyar da jama’a su sami bunƙasa.”

“A taƙaicen-taƙaitawa, mun ƙuduri aniyar yin jagoranci na gari,” a cewar Sanata Kashim Shettima.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *