Daga MUKHTAR YAKUBU, a Kano
A yanzu haka dai ta tabbata jarumin Kannywood Abdullahi Amdaz ya zama mai igiya biyu.
Amdaz ya kara aure a ranar Asabar, 30 ga Disamba, 2023 a garin Maiduguri, Jihar Barno
An daura auren Abdullahi Amdaz da abar kaunar sa A’isha Umar Timta da misalin karfe 11:00 na safe a gidan sarkin Gwoza da ke kan Titin Gombale, kusa da makarantar Capital, Giwa Barrack, Maiduguri, Jihar Barno.
Allah ya ba su zaman lafiya da zuria dayyiba.
