Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Marigayi Yahaya Adamu, Shugaban Sashen Buga Jaridun Blueprint.
Ministan ya bayyana marigayin a matsayin ma’aikaci mai himma da gaskiya, inda rasuwarsa ta kasance babban rashi mai raɗaɗi a zuciya.
Idris, wanda ya ɗage wata ganawa ta aiki domin wannan ziyara a Kaduna, ya ce marigayin ya samu girmamawa daga jama’a saboda halinsa na kirki da jajircewa wajen aikin sa.
Ya yi addu’a da cewa: “Allah Maɗaukakin Sarki Ya sa mutuwa ta zama ga marigayin, ya gafarta masa kurakuransa.”
Haka zalika, Shugaban kamfanin jaridun Blueprint, Mallam Salisu Umar, ya bayyana cewa marigayi Yahaya Adamu, “ya wuce ma’aikaci a wurina; aboki ne, kuma ginshiƙi ne a ayyukanmu.”
Umar ya bayyana hakan ne yayin ziyarar ta’aziyya da ya kai gidan iyalan marigayin a Kaduna, inda ya ce rasuwar Yahaya ta bar babban giɓi a zuciyarsa da kuma a tsarin aiki na kamfanin.
Ya ce, Malam Yahaya mutum ne mai aiki tuƙuru, mai jajircewa, wanda ba ya wasa da nauyin da aka ɗora masa.
Ya ƙara da cewa, kamfanin ya rasa mutum mai muhimmanci, wanda kowa ke girmamawa saboda halayensa na kirki da kwarewa.
Mallam Salisu Umar ya yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki ya yafe masa kurakuransa, ya ba shi gurbi a cikin Aljannatul Firdaus, tare da ba iyalansa haƙuri da juriyar rashinsa.
Marigayi Yahaya Adamu ya rasu ne da safiyar Asabar a Kaduna bayan rashin lafiya da ya yi fama da ita na ‘yan kwanaki.
Bayan dawowa daga asibiti, yanayinsa ya sake tabarbarewa, lamarin da ya tsoratar da iyalai da abokansa.
Daga cikin masu kai ziyarar ta’aziyya akwai Alhaji Ibrahim Sheme, ɗaya daga cikin manyan daraktocin Blueprint, wanda shi ma ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai nutsuwa da bin doka a aikinsa.
A wata sanarwa da Nuhu Sani daga sashen Harkokin Ma’aikata da Gudanarwa na kamfanin ya rattaba hannu, kamfanin ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi da ya girgiza kowa a kamfanin.
Ya ce, jana’izar ta gudana ne a unguwar Kabala Costain da ke Kaduna, bisa ƙa’idojin addinin Musulunci.
Babban ɗan marigayin, Adamu Yahya, ya shaida wa Blueprint cewa mahaifinsu ya dade yana ƙorafi kan ciwon ƙirji tsawon kusan makonni biyu kafin jikinsa ya kai ga yin rauni sosai.
Ya ce su iyalai sun shiga babban tashin hankali da alhini saboda rasuwar wane da suka dogara da shi.
Marigayi ya bar mata ɗaya da ‘ya’ya goma, bayan barin tarihi na aiki mai kyau da zamantakewa nagari da kowa ke yaba wa.
Jana’izar tasa ta ja hankalin jama’a da dama — abokai, makwabta, da ma’aikatan Blueprint — waɗanda suka halarta domin yi masa addu’a a makabartar Kabala, inda aka roƙi Allah ya jiƙansa ya kuma ba iyalan sa ikon jurewa wannan babban rashi.
