Editor

9045 Posts
An damƙe mutum biyu bisa zargin kashe ɗan jarida, Hamisu Danjibga a Zamfara

An damƙe mutum biyu bisa zargin kashe ɗan jarida, Hamisu Danjibga a Zamfara

'Yan sanda a Jihar Zamfara sun damƙe wasu mutum biyu da ake zargi da kashe ɗan jarida Hamisu Danjibga a jihar. Kwamishinan 'Yan Sandan Jihar, Mohammed Dalijan, ya ce ana zargin wani ɗan ɗan'uwan marigayin, Mansur Haruna tare da abokinsa Ibrahim Nababa su ne suka kashe ɗan jaridar. Kwamishinan ya bayyana haka ne a ranar Talata a lokacin da aka baje waɗanda ake zargin a Hedikwatar 'Yan Sanda da ke Gusau, babban birnin jihar. Ya ce an kama waɗanda ake zargin ne bayan da jami'ansu suka sunkuya bincike biyo bayan kashe marigayin. A cewar Kwamishinan, "Babban wanda ake zargi shi…
Read More
Arewa ina mafita? Ya kamata mu farka daga barci ‘yan Arewa!

Arewa ina mafita? Ya kamata mu farka daga barci ‘yan Arewa!

Daga ABDULLAHI JIBRIL LARABI Hasbinallahu Wa Ni'imal Wakil! 'Yan bindiga sun kwashi mata a Federal University Dutsen-Ma. Mako biyu da suka wuce sun kwashi mata a Federal University Gusau. Wannan wace irin masifa ce take neman mamaye Arewa? Shin haka za mu zauna mu zuba ido don abin ba akanmu yake faruwa ba ko a kan Makusantanmu? Ina manyan malamanmu na addini? Ba za a ji muryoyinsu ba sai akan saɓanin aƙida ko siyasa? Shin ina manyan yan siyasar Arewa? Sai lokacin Kamfe za su san da zamanmu kenan?Ina manyan sarakunanmu na Arewa? Sai lokacin bukukuwan Sallah za a ji…
Read More
Ina ma Atiku zai ji shawarata..!

Ina ma Atiku zai ji shawarata..!

Daga RAHMA ABDULMAJID Kamar yadda 'yan ƙasa suka sani, tsohon mataimakin tsohon Shugaban ƙasar Nijeriya Alhaji Atiku Abubakar ya narka kuɗi da lokaci wajen neman Jami'ar Chicagon Amurka da ta bayyana sakamakon karatun Shugaban Nijeriya mai ci wato Bola Ahmed Tinubu, Inda a daren Litinin ne Jami'ar ta amsa buƙatar da wasu dogayen takardu wanda a dunƙule suke gaskata cewa Shugaba Tinubu ɗalibinta ne, amma ba huruminta ba ne adana kwafi na shahadar calibai ba balle ma ɗaliban tale-tale 'yan 70s ba tunda tuni ta ba su abinsu. A yayin da 'yan Nijeriya suka rabu biyu wasu na murna da…
Read More
Karatun ta nutsu daga masu rawar kai

Karatun ta nutsu daga masu rawar kai

Daga ƊANLADI Z. HARUNA Lokacin da na ji labarin an cafke yarinyar nan Fiddausi mai ƙunduma ashariya da barazanar ta da bom ga wasu manya ban yi mamaki ba. Na tabbatar da ƙwarewar jami'an tsaron Nijeriya musamman ma DSS kan abin da suka sa kansu. Ƙwarewar jami'an tsaron Nijeriya ta wuce sanin irin mu 'yan koko-ciko, karan kaɗa miya. Sai dai kuma wannan balahira ta sa na ƙara yin amanna da wasu abubuwa kamar haka: Na ɗaya, kamar yadda na faɗa, jami'an tsaron Nijeriya suna da qwarewa da matuƙar iya bincike ga abin da suka ga damar ƙaddamarwa. Na sha…
Read More
Gwamna Dikko ya ƙaddamar da dakarun tsaron al’umma a Katsina

Gwamna Dikko ya ƙaddamar da dakarun tsaron al’umma a Katsina

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya ƙaddamar da Dakarun Tsaron Al'umma na Jihar Katsina (Katsina Community Watch Corps) gami da muhimman kayan aiki domin dawo da tsaro a faɗin jihar. Shafin Katsina Post ya rawaito cewa an gudanar da bikin ƙaddamawar ne a babban filin wasa na Muhammadu Dikko da ke cikin birnin Katsina ranar Talata. Kalika, bayan ƙaddamar da dakarun su 1,500, Gwamnan jihar ya kuma ƙaddamar da motoci masu sulke ƙirar Hilux guda 70 da kuma babura 700 domin yaƙi da ta’addanci a lungu da saƙo na jihar Katsina. Taron ya samu halartar fitattun mutane da shugabannin…
Read More
Ƙabilar Kibishi: Masu banƙare wa budurwa leɓe da sunan ado

Ƙabilar Kibishi: Masu banƙare wa budurwa leɓe da sunan ado

Masu iya magana na cewa "Allah ɗaya, gari bamban". Su dai waɗannan bayin Allah suna rayuwa ne a yammacin kogin ‘Omo’ da ke kudu-maso-yammacin Habasha, ana kiransu da ‘Kibishi’. Bincike ya nuna cewa su dai waɗannan mutane makiyayane, sannan a kan gane yawan dukiyar kowane gida ta hanyar la’akari da yawan dabbobin da suka mallaka. Addini: Waɗannan mutane suna da abin bauta wanda suke yi masa laƙabi da ‘Tuma’. Sun yi imani cewar shi dai wannan Tuma ya kasancene a cikin sararin samaniya, bugu da ƙari mutanen sun yi imani da al’matsutsai da kuma ifiritai, sun kuma yi imani da…
Read More
Me ya sa mata ke canzawa bayan aure?

Me ya sa mata ke canzawa bayan aure?

Tare da AMINA YUSUF ALI Barkanmu da sake haɗuwa a wani makon a shafin ma'aurata na zamantakewa. A wannan mako mun zo da jawabi a kan yadda mata suke canzawa bayan aure. Kamar yadda wani makarancin wannan filin ya yi min ƙorafin cewa, wai me ya sa ba za a ja kunnen a kan mata su daina canzawa bayan aure ba? Domin a cewar sa, mace tana canzawa daga yadda aka aure ta. Wato ta sauya daga yarinyar kirki mai hankali da biyayya da sanin ya kamata, zuwa mara kunya, mara kulawa, mara biyayya, da sauransu dai. Ba kamar dai…
Read More
NiMet ta yi hasashen yiwuwar samun ruwan sama mai ƙarfi a wasu jihohi

NiMet ta yi hasashen yiwuwar samun ruwan sama mai ƙarfi a wasu jihohi

Hukumar Hasashen Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta fitar da sanarwa mai ɗauke da hasashen yiwuwar samun ruwan sama mai ƙarfi a jihohi da dama a cikin wannan makon. Ga abin da hasashen NiMet ya nuna kamar haka: Hasashen ranar Talata: Ana sa ran samun ruwan sama mai ƙarfi a wuraren da suka haɗa da jihohin Delta, Bayelsa, Rivers, Imo, Anambra, Akwa lbom, Cross River, Oyo, Ogun, Osun, Ekiti, Kogi, da kuma Ondo. Sannan ana sa ran samun ruwan sama matsaikaici zuwa ƙasa a jihohi da suka haɗa da FCT, Kaduna, Filato, Nasarawa, Kwara, Edo, Abia, sai kuma Taraba. Yayin da…
Read More
NECO ta bayyana lokacin fitar da sakamakon jarrabawar SSCE na 2023

NECO ta bayyana lokacin fitar da sakamakon jarrabawar SSCE na 2023

A wannan Talatar ake sa ran Hukumar Shirya Jarrabawa ta Ƙasa (NECO), ta fitar da sakamakon jarrabawar da ɗaliban da suka kammala sakandare suka rubuta na 2023. Wannan na zuwa ne bayan shafe dogon lokaci ɗalibai da iyayensu na dakon sakamakon domin ganin sakamakon da aka samu. Sai dai da alama jinkirin da aka samu wajen fitar da sakamakon na haifar da cikas wajen ɗaukar sabbin ɗalibai a jami'o'i da ma sauran manyan makarantu. Kuma hakan ya haifar da ɗar-ɗar ga ɗaliban da ma iyayen nasu. Tun bayan kammala jarrabawar a farkon watan Agustan da ya gabata, NECO ta yi…
Read More
Shugabancin Bayelsa: Kotu ta soke cancantar shiga takarar ɗan takarar APC, Sylva

Shugabancin Bayelsa: Kotu ta soke cancantar shiga takarar ɗan takarar APC, Sylva

Babbar Kotun Tarayya mai zamanta a Abuja, ta soke cancantar shiga takara ta ɗan takarar jam'iyyar APC, Cif Timipre Sylva, a zaɓen gwamnan jihar Bayelsa mai zuwa. A ranar Litinin kotun a ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Donatus Okorowo, ta yanke wannan hukuncin. Ya zuwa ranar 11 ga watan Nuwamban 2023 ne ake sa ran gudanar da zaɓen gwamna a jihar ta Bayelsa. Alƙalin ya ce tun da an taɓa rantsar da Sylva sau biyu a matsayin gwamnan jihar kuma ya yi mulki na tsawon shekara biyar, sake shiga takarar gwamna a jihar hakan ya saɓa wa Kundin Tsarin Mulki na…
Read More