11
Oct
'Yan sanda a Jihar Zamfara sun damƙe wasu mutum biyu da ake zargi da kashe ɗan jarida Hamisu Danjibga a jihar. Kwamishinan 'Yan Sandan Jihar, Mohammed Dalijan, ya ce ana zargin wani ɗan ɗan'uwan marigayin, Mansur Haruna tare da abokinsa Ibrahim Nababa su ne suka kashe ɗan jaridar. Kwamishinan ya bayyana haka ne a ranar Talata a lokacin da aka baje waɗanda ake zargin a Hedikwatar 'Yan Sanda da ke Gusau, babban birnin jihar. Ya ce an kama waɗanda ake zargin ne bayan da jami'ansu suka sunkuya bincike biyo bayan kashe marigayin. A cewar Kwamishinan, "Babban wanda ake zargi shi…