Editor

9513 Posts
Marubutan Arewa sun yi taron alhinin rasuwar Sheikh Yusuf Ali

Marubutan Arewa sun yi taron alhinin rasuwar Sheikh Yusuf Ali

DAGA MUKHTAR YAKUBU An bayyana fitaccen malamin addinin Musluncin nan marigayi Sheikh Dakta Yusuf Ali wanda Allah ya yi wa rasuwa a farkon watan Nuwamban da ya gabata a matsayin wani managarcin malamin da ya yi shaharar da za a daɗe ba a manta da shi ba a fannin ilimi da kuma mu'amala da jama'a Wannan bayanin ya fito ne daga bakin shugaban majalisar malamai ta Arewa da kuma ta Jihar Kano Sheikh Ibrahim Khalil a lokacin da yake gabatar da jawabin sa a wani taro da gamayyar ƙungiyar marubutan Arewa da ƙungiyar ANA ta ƙasa reshen Jihar Kano suka shirya…
Read More
Gwamnan Zamfara ya jajanta wa al’ummar Zurmi bisa harin ‘yan bindiga, ya jinjina wa jami’an tsaro

Gwamnan Zamfara ya jajanta wa al’ummar Zurmi bisa harin ‘yan bindiga, ya jinjina wa jami’an tsaro

Gwamna Dauda Lawal ya jajanta wa al’ummomin da hare-haren ‘yan bindiga ya shafa a baya-bayan nan, ya kuma yaba wa sojoji bisa kokarinsu. Akwai rahotanni masu kyau da yawa na kawar da dimbin ‘yan bindiga a Zamfara da sauran dazuzzukan Arewa maso Yamma. A wata sanarwa da mai magana da yawun sa, Sulaiman Bala Idris ya fitar, gwamna Lawal ya nuna matuƙar damuwarsa kan hare-haren da aka kai a karamar hukumar Zurmi. Ya ce duk da hare-haren da ‘yan bindigar ke kai wa, rahotanni masu inganci sun nuna an kawar da fitattun shugabannin ‘yan bindigar da ke aiki a jihar…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnati ta amince da cire jami’o’i da takwarorinsu daga tsarin biyan albashi na IPPIS

Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnati ta amince da cire jami’o’i da takwarorinsu daga tsarin biyan albashi na IPPIS

Daga BASHIR ISAH Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC), ta amince da cire jami'o'i da sauran manyan makarantun ƙasar nan daga tsarin biyan albashi na bai-ɗaya, IPPIS. Da wannan, yanzu makarantun da lamarin ya shafa su da kansu za su riƙa kula da biyan albashin ma'aikatansu. Ministan Ilimi, Farfesa Mamman Tahir, shi ne ya bayyana haka ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala zaman majalisar a ranar Laraba a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja. Ya ce gwamnati ta yanke shawarar cire manyan makarantu daga tsarin biyan albashi ns IPPIS ɗin ne saboda damuwa da son ganin harkokin makarantun suna gudana…
Read More
Rashin lafiyar Gwamnan Ondo ya haifar da naɗa Mataimaki muƙaddashi

Rashin lafiyar Gwamnan Ondo ya haifar da naɗa Mataimaki muƙaddashi

Daga BASHIR ISAH Majalisar Dokokin Jihar Ondo ƙarƙashin jagorancin Kakinta, Olamide Oladiji, ta ayyana Mataimakin Gwamnan Jihar, Lucky Aiyedatiwa a matsayin muƙaddashin gwamna. Hakan ya biyo bayan wasiƙar da majalisar ta ce ta samu ne daga Gwamnan Jihar, Oluwarotimi Akeredolu, kan buƙatar miƙa ragamar mulkin jihar ga mataimakimsa kasancewar zai tafi hutun jinya. A ranar Laraba, Kakakin majalisar ya ayyana Aiyedatiwa a matsayin muƙaddashin gwamnan jihar a Akure, babban birnin jihar. A cikin sanarwar da ya yi a zauren majalisar, Kakakin ya ce: “Biyo bayan shawarar da likita ya bayar ta buƙatar zuwa duba lafiyarsa, Gwamnan Jihar Ondo, Oluwarotimi Odunayo…
Read More
Tonon Silili: Da hannun wasu ‘manyan ƙasa’ cikin ɗaukar nauyin ‘yan ta’adda a Nijeriya, in ji Minista

Tonon Silili: Da hannun wasu ‘manyan ƙasa’ cikin ɗaukar nauyin ‘yan ta’adda a Nijeriya, in ji Minista

Daga BASHIR ISAH Ministan Ma'adinai, Mr Dele Alake, ya bayyana cewa da hannun wasu manyan ƙasa a harkar ɗaukar nauyin 'yan ta'adda da haƙar ma'adinai ta ɓarauniyar hanya a Nijeriya. Jaridar News Point Nigeria ta rawaito cewar, Alake ya yi wannan tonon sililin ne sa'ilin da ya bayyana a gaban Kwamitin Majalisar Wakilai Kan Ma'adinai don kare kasafin ma'aikatarsa na shekarar 2024 a Abuja. Kazalika, Ministan ya yi zargin akwai baƙi da ke haƙar ma'adinai a Nijeriya ba bisa ƙa'ida ba. Don haka ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta maida hankali sosai kan fannin ma'adinai wanda ka iya samar wa…
Read More
Babu dimukraɗiyya a Nijeriya

Babu dimukraɗiyya a Nijeriya

Daga NAFIU SALISU Idan a na batu na mulkin Dimokraɗiyya da alfanunta a ƙasashen da suke tafiyar da ita Dimokraɗiyyar, to za mu iya cewa ba za a taɓa saka ƙasata Nijeriya ba, domin babu ita a jerin ƙasashen da suka cancanci a kira 'yan ƙasar masu rayuwa a ƙarƙashin mulkin Dimokraɗiyya. Wannan kuma ta faru ne dalilin rashin tafiyar da dimokraɗiyyar a yadda take, da kuma tsarin da ake tafiyar da ita a ƙasa. Dimokraɗiyya dai ita ce, Gwamnatin al'umma domin al'umma, wato Gwamnatin da al'ummar ƙasa suka kafa domin ita kanta al'ummar don rayar da mutane su ci…
Read More
Gwamnatin Zamfara ta kammala kashi na biyu na shirin kula da lafiya kyauta

Gwamnatin Zamfara ta kammala kashi na biyu na shirin kula da lafiya kyauta

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Jihar Zamfara ta kammala kashi na biyu na shirin kula da lafiyar al'ummar jihar kyauta da ta faro. Sanarwar da mai magana da yawun Gwamna, Sulaiman Bala Idris ya fitar ta ce, a watan Agustan da ya gabata kashin farko na shirin kula da lafiya kyautar ya kankama inda aka yi wa masu fama da lalurori daban-daban magani ba tare da sun biya ko taro ba. Idris ya ce mutum 1,858 ne aka samu nasarar yi musu magani a tsakanin kashin farko da na biyu na shirin. Ya ƙara da cewa, an fara kashi na biyu…
Read More
Hanyoyin da za su taimaka wurin daɗewa a mu’amalar aure

Hanyoyin da za su taimaka wurin daɗewa a mu’amalar aure

Tare da AMINA YUSUF ALI Gabatarwa: Bismillahir Rahmanir Rahim. Maza da yawa suna fama da matsalar kawowa da wuri, ko sun yi magana ko ba su yi magana ba, ya kasance ɗaya daga cikin jirinjiritsin da maza ke fuskanta lokacin mua'amalar aure. Kawowa da wuri shi ne lokacin da namiji ya yi inzali da wuri fiye da yadda ake tsammani ko kuma wasu lokuta (mafi yawa mintuna 2) bayan fara mu'amalar aure. Wasu lokutan inzali da wuri yana faruwa ne saboda rashin ƙwarewa, rashin shiri, rashin lafiya, ko kura-kurai da za a iya kauce wa yayin saduwa. Wannan babbar damuwa…
Read More
Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 17,000 a cikin kwana 62

Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 17,000 a cikin kwana 62

Daga BASHIR ISAH Falasɗin ta bayyana cewa, Isra'ila ta kashe sama da mutum 17,000 a Gaza a cikin kwana 62 a ci gaba da gwabza yaƙi a tsakanin ƙasashen biyu. Falasɗin ta ce daga cikin wannan adadi, 7,224 ƙanan yara ne, sai kuma mata 5,818, tsofoffi 478, jami'an kiwon lafiya 281, 'yan jarida 77, sai kuma mutum 46,000 da suka jikkata. Ta ƙara da cewa, a bayyana ne cewa galibin waɗanda faɗan ya fi shafuwa mata da ƙananan yara ne. Waɗannan bayanai na ƙunshe ne cikin sanarwar manema labarai da ƙasar Falasɗin ta fitar mai ɗauke da kwanan wata 11…
Read More
Asalin Kaduna daga tushe

Asalin Kaduna daga tushe

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Zagayen wani kogi da ake kira Kadduna, akwai wasu ƙauyuka da mutane ke zaune warwatse a gurin. Daga cikin irin waɗannan jama'a akwai ƙabilu da suka fi yawa kamar irin su Gbagyi wanda Bahaushe yake kira Gwari, da kuma Fulani. Gwarawa na zaune a ƙauyen Kudanda, wanda yanzu ya zama Kakuri, Fulani kuma ta nasu ɓangaren suna zaune a Kukogi wanda yanzu ta koma Gworo. Wannan kogi matattara ce ta kadoji wanda hakan ta jawo ake kiran sa da suna Kadduna, ita kuma wannan kalma ta Kadduna, jama'un kalmar kada ce, wacce ma'anarta ita ce kadodi…
Read More