09
Nov
Daga BASHIR ISAH Shugaban Kwamitin Wanzar da Zaman Lafiya na Ƙasa, Janar Abubakar Abdulsalami (rtd), ya yi kira ga jam'yyun siyasa da magoya bayansu da a guji nuna halin a-yi-rai-ko-a-mutu yayin zaɓen gwamnonin da za a gudanar ranar Asabar a jihohin Bayelsa da Kogi da kuma Imo. Abdulsalami ya yi wannan kira ne yayin da jam'iyyin siyasa su 18 da za su fafata a zaɓen gwamna a Jihar Kogi suka rattaɓa hannun kan yarjejeniyar zaman lafiya ranar Laraba a jihar. Da yake jawabi ta bakin wakilinsa Cardinal John Onaiyekan, tsohon shugaban ƙasar ya ce: “Wannan taro na da muhimmanci saboda…