Editor

9513 Posts
Yadda aka gudanar da bajekolin finafinai na KILAF 2023 a Kano

Yadda aka gudanar da bajekolin finafinai na KILAF 2023 a Kano

Daga MUKHTAR YAKUBU  A ranar Talatar makon jiya  ne aka fara bikin kalankuwa ko bajekoli na Afirka mai suna 'Kano Indigenous Languages of  Africa Film  Market and Festival', wato KILAF a taƙaice da a ka yi wa na bana laƙabi da ‘KILAF AWARD 2023’, wanda kuma shi ne karo na shida da aka gudanar tun daga lokacin da aka fara shi a 2018. An kammala taron a ranar Asabar 26 ga Nuwamba, 2023, da bikin bayar da kyautuka na gasa da a ka yi na harsunan Afirka bayan kwanaki biyar da aka kwashe ana gudanar da bikin wanda na farko…
Read More
Tinubu ya yi matuƙar damuwa kan iftila’in Tudun Biri – Malagi

Tinubu ya yi matuƙar damuwa kan iftila’in Tudun Biri – Malagi

Daga BASHIR ISAH Ministan Labarai da Wayar da Kan 'Yan Ƙasa Mohammed Idris, ya bayyana cewa, Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya nuna damuwa matuƙa kan iftila'in da ya auku a yankin Tudun Biri, Jihar Kaduna inda sojoji suka jefa wa masu taron maulidi bom bisa kuskure. Hadimin Ministan, Rabiu Ibrahim, ya bayyana a cikin sanarwar da ya fitar ranar Litinin cewa, Malagi ya bayyana haka ne a wajen taron Babban Kwamitin Shugabancin Jama’atu Nasril Islam (JNI) da ya gudana ran Litinin a Minna, babban birnin Jihar Neja. Ministan ya nuna godiyar gwamnatin ga sarakunan gargajiya da shugabannin addini bisa ƙoƙarin…
Read More
Fannin kare haƙƙin ɗan-Adam na buƙatar jajirtattun mutane – MƊD

Fannin kare haƙƙin ɗan-Adam na buƙatar jajirtattun mutane – MƊD

Sakatare-Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Guterres ya jaddada ƙa'ida cewa, “an haifi kowani ɗan Adam da ‘yanci kuma suna da mutunci da haƙƙi." Guterres ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa don cika shekaru 75 da ƙaddamar da yarjejeniyar kula da haƙƙoƙin bil’adama na duniya a ranar 10 ga Disamba 2023. Ya ce, “Yarjejeniyar Haƙƙin ɗan-Adam ta Duniya tana da mahimmanci a yau kamar yadda take a lokacin da aka amince da ita shekaru 75 da suka gabata. “Yarjejeniyar duniya taswirar hanya ce, tana taimaka wa kawo ƙarshen yaƙe-yaƙe da haɓaka rayuwar zaman lafiya da mutunci ga duka…
Read More
Dandalin shawara: Ina neman dabarun da saurayina zai dinga ba ni kuɗi ko ba yawa

Dandalin shawara: Ina neman dabarun da saurayina zai dinga ba ni kuɗi ko ba yawa

Daga AISHA ASAS  TAMBAYA: Assalamu alaikum. Aunty Aysha, ya ki ke? Ya yara? Don Allah shawara na ke so a ba ni. Ina da saurayi, yana so na, ni ma kuma Ina son shi, ga shi iyaye na sun matsa min akan na fito da miji nai aure. Ni kuma na kasa gaya mai yanzu haka wancan sati akai auren ƙanwata yanzu sun ce in ban fito da miji nan da wata ɗaya ba, duk wanda suka zaɓa min shi zan aura. Ni kuma Ina son wancan, amma na kasa gaya mai, kuma shi wanda nake so bai ban kosisin…
Read More
CBN ya dakatar da cajin da bankuna kan yi wa kostomomi yayin ajiyar kuɗaɗe

CBN ya dakatar da cajin da bankuna kan yi wa kostomomi yayin ajiyar kuɗaɗe

Daga BASHIR ISAH Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya dakatar da harajin da akan karɓa yayin da kostomomi suka kai kuɗi mai yawa ajiya a banki. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Muƙaddashin Daraktan Sanya Ido, Dr Adetona Adedeji, ya fitar a ranar Litinin. “Dukkanin bankunan da ke ƙarƙashin kulawar CBN su ci gaba da karɓar ajiyar kostomominsu ba tare da sun caje su komai ba," in ji CBN. Bankin ya kuma buƙaci bankuna da su bi wannan umarnin nasa sau da ƙafa. Sanarwar ta ce sabuwar dokar da aka samar a Disamban 2019, mai lamba FPR/DIR/GEN/CIR/07/042, ita ce ta…
Read More
Sarkin Katsina bai kori shirin AGILE a jihar ba

Sarkin Katsina bai kori shirin AGILE a jihar ba

Daga UMAR GARBA a Katsina A ƙarshen makon da ya gabata wasu kafafen yaɗa labarai sun ruwaito cewar, Mai Martaba Sarkin arkin Katsina, Alhaji Abdulmumin Kabir Usman, ya kori shirin nan da ke inganta ilimin 'ya'ya mata wato AGILE a taƙaice, a wasu jihohin ƙasar nan ciki har da jihar Katsina. Lamarin ya jawo cece-kuce musamman a kafafen sada zumunta bayan da wani babban malami da wasu jama'ar arewacin ƙasar nan suka zargi shirin da lalata tarbiyyar 'yan mata ta hanyar koya masu wasu ɗabi'u da ka iya sa 'yan matan su bijire wa addini da ma al'ada. Sarkin labarai…
Read More
Mutanen Tudun Biri sun yi shahada, in ji Shugaba Tinubu

Mutanen Tudun Biri sun yi shahada, in ji Shugaba Tinubu

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sake nuna baƙin cikin sa kan harin bom da ya kashe mutane a garin Tudun Biri. Ya kuma yi wa mamatan fatan samun shahada. Da yake jawabi a Masarautar Maiduguri a ziyarar da ya kai Jahar borno don halartar taron Chief of Army Staff Conference a yau litinin Shugaban ya ce: "Har yanzu ina ƙara jaddada mana ta'aziyya kan asarar rayukan da muka yi a Kaduna, abin babu dadi Sam, amma a matsayin mu na mutanen da suka yi imani da ƙaddara dole mu karɓi wannan lamari a matsayin ƙaddara, sannan mu jajirce wajen…
Read More
Ta ya ake iya gane namiji na ɗauke da ciwon sanyi?

Ta ya ake iya gane namiji na ɗauke da ciwon sanyi?

Daga AISHA ASAS Mai karatu barkanmu da sake ganin zagayowar sati lafiya. Har wayau dai muna nan kan maudu'in namu na ciwon sanyi. Idan kana tare da mu, darasin namu ya soma ne tun daga ma'anar ciwon sanyi, yadda yake samuwa, yadda ake iya kaucewa samuwar shi, wasu ɗabi’u da muke yi da ke kai mu ga ciwon, matsayin sanya kayan ƙamshi a farji, alaƙar kayan mata da ciwon sanyi, da sauransu. A wannan makon, shafin Kwalliya na jaridar Blueprint Manhaja zai waiwayi maza a matsala ta ciwon sanyi, na sani da yawa za su ji wannan darasi a matsayin…
Read More
Za a iya amfani da Zakkat da Waƙafi a yaƙi da talauci a Nijeriya – AZAWON

Za a iya amfani da Zakkat da Waƙafi a yaƙi da talauci a Nijeriya – AZAWON

Daga MUKHTAR A. HALLIRU TAMBUWAL a Dutse Shugaban ƙungiyar Hukumomi da ƙungiyoyin da ke aikin tattara Zakka da Waƙafi a Nijeriya, AZAWON, Malam Muhammad Lawal Maidoki, ya bayyana cewa, matuƙar za a yi amfani da kuɗaɗen da ake tattarawa daga Zakka da Waƙafi da sadakoki da masu hannu da shuni ke fitarwa, domin yaƙi da talauci, yunwa, da ƙuncin rayuwa da ake fuskanta a ƙasar nan. Malam Muhimmad Lawal Maidoki (Sadaukin Sokoto) ya bayyana haka ne a yayin ƙaddamar da fara babban taron haɗaɗɗiyar ƙungiyar AZAWON ta ƙasa karo na 3, a garin Dutse, Babban Birnin Jihar Jigawa. A cewarsa,…
Read More
Ƙaruwar matsalar lalata da ɗalibai a jami’o’in Nijeriya

Ƙaruwar matsalar lalata da ɗalibai a jami’o’in Nijeriya

Ga duk mai bibiyar al’amuran da suka shafi shafin yanar gizo, ko kuma mu ce harkar yaɗa labarai a ƙasar nan ya san yadda a ’yan watannin nan ake yawan samun koke-koken game da yadda wasu malaman jami’o’i ke lalata da ɗalibansu don su ba da maki, ko kuma don a kai su inda ba su kai ba a harkar jarrabawa. Ko ba a ce komai ba, wannan wani mummunan abu ne da za a iya cewa bai kama da hakali ba, ko kuma mu ce wani abu ne da ya zama bala’in wanda idan ba a yi hankali ba…
Read More