Editor

9513 Posts
Fitacciyar ma’aikaciyar NTA, Aisha Bello ta kwanta dama

Fitacciyar ma’aikaciyar NTA, Aisha Bello ta kwanta dama

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi wa fitacciyar ma'aikaciyar tashar talabijin ta tarayyar (NTA), Aisha Bello Mustapha, rasuwa. A ranar Lahadi Aisha ta rasu amma sai a Litinin aka yaɗa batun rasuwar wanda ya zuwa haɗa wannan labari ba a bayyana abin da ya yi ajalin marigayiyar ba. A halin rayuwarta, marigayiyar ta yi fice musamman a fagen karanta labatai a tashar NTA. 'Yan ƙasa da dama sun bayyana kaɗuwarsu game da Aisha duba da irin gudunmawar da ta bayar ga ɓangaren yaɗa labarai. Da misalin ƙarfe ɗaya na ranar Litinin aka yi wa marigayiyar sallar janaza a Babban Masallacin…
Read More
Shugabanci nagari ne kaɗai hanyar magance matsalar juyin mulki – ECOWAS

Shugabanci nagari ne kaɗai hanyar magance matsalar juyin mulki – ECOWAS

Shugaban Ƙungiyar ECOWAS, Bola Tinubu, ya roƙi shugabannin ƙasashen yammacin Afirka da su ba da fifiko wajen gudanar da shugabanci nagari da samar da walwalar jama’a, a matsayin wani muhimmin makamin yaƙar juyin mulki a yankin. Da yake jawabi a wajen taron ECOWAS karo na 64 da ya gabata a ranar Lahadi, shugaban ya bayyana gudanar da shugabanci nagari a matsayin wani babban ginshiƙi na samar da goyon bayan jama'a ta hanyar kawo sauyi ga al'umma da tattalin arziki da cigaban yammacin Afirka. “Samar da shugabanci nagari ba wai kawai zallar nasarar samin shugabanci ba ce, hanya ce ta magance…
Read More
Tudun Biri: Sanatoci sun sadaukar da albashinsu na wata guda ga waɗanda harin bom ya shafa

Tudun Biri: Sanatoci sun sadaukar da albashinsu na wata guda ga waɗanda harin bom ya shafa

Daga BASHIR ISAH Baki ɗayan sanatocin Tarayyar Nijeriya su 109 sun yanke shawarar sadaukar da albashinsu na wata guda da ya kai Naira miliyan 109 ga waɗanda iftila'in harin bom ya shafa a Tudun Biri, cikin Ƙaramar Hukumar Igabi, Jihar Kaduna. Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin ne ya bayyana haka ranar Lahadi a Fadar Gwamnatin Jihar Kaduna yayin da ya jagoranci tawagar Majalisar Dattawa zuwa jihar don miƙa ta'aziyya da kuma jajantawa. Gwamnan Jihar, Sanata Uba Sani, shi ne ya tarbi tawagar yayin ziyarar. Cikin sanarwar da ya fitar ta hannun hadiminsa Ismail Mudashir, Sanata Barau ya ce…
Read More
Kisan masu mauludi: Za a hukunta masu hannu ciki – Tinubu

Kisan masu mauludi: Za a hukunta masu hannu ciki – Tinubu

*A na cigaba da tir da kisan ’yan mauludi a Kaduna*Za mu biya diyya, inji Gwamnatin Tarayya *Fasahar zamani za ta rage tashin boma-bomai – Amurka ga sojojin Nijeriya Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar wa al’ummar ƙasar cewa duk wanda aka samu da hannu a harin bom da aka kai ƙauyen Tudun Biri wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 90 za a hukunta shi. Shugaban Ƙasar ya kuma bayar da tabbacin cewa, za a kula da duk waɗanda abin ya shafa a ƙarƙashin shirin tallafi na Folako Initiative da za a…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta ci burin ninninka kuɗin fetur zuwa Naira tiriliyan 7.69 a shekarar 2024

Gwamnatin Tarayya ta ci burin ninninka kuɗin fetur zuwa Naira tiriliyan 7.69 a shekarar 2024

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnatin Tarayya ta ci burin ninninka kuɗaɗen shiga da take samu ta hanyar man fetur har ninki uku wato zuwa Naira tiriliyan 7.69 a shekarar 2024 domin ta samu damar cikashe wani vangare na kasafin kuɗin ƙasa na shekarar 2024 wanda ya kai har kimanin Naira triliyan 27.5. A cewar wani lissafi da hasashe a game da gabatar da daftarin ƙudurin kasafin kuɗin ƙasar nan na 2024 wanda ministan kasafin kuɗi da tsare-tsaren tattalin arziki, Abubakar Atiku Bagudu ya gabatar, ya nuna cewa hasashen kuɗin shigar da za a samu a ɓangaren man fetur a 2024…
Read More
Rahoton bincike: Jihohi 10 da suka yi zarra wajen cin bashi a Nijeriya

Rahoton bincike: Jihohi 10 da suka yi zarra wajen cin bashi a Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI A cikin shekarar bana ta 2023 Nijeriya ta fuskanci ƙalubale da dama da yake da alaƙa da tattalin arzikin ƙasar. Wannan dalili ya sa wasu jihohi da dama a Nijeriya suka dulmiya tsundum a cikin tarkon bashi. Jaridar Ingilishi ta The Spectacles ta yi bincike da nazari a kan wasu jihohi guda 10 da suka fi kowaɗanne ciyo bashi a Nijeriya. Legasa (Naira triliyan 1.97) Ta farko a cikin jerin ita ce jihar Legas wacce take a Kudancin Nijeriya. Jihar Legas ta jagoranci wannan jeri ne na jihohi masu kan bashi ne saboda bashin da ta…
Read More
Bom ɗin Tudun Biri ya jawo matuƙar juyayi

Bom ɗin Tudun Biri ya jawo matuƙar juyayi

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Haka rayuwa ta ke wataran a na kuka wataran a yi dariya amma gaskiya a yanayin da Nijeriya ke ciki mafi rinjaye ko ba kukan a ke yi ba to ba dai dariya a ke yi ba. Duk ƙaddarar da ta yi mai kyau ko mummuna sai a maida lamari ga Allah. Ɗan-adam ba shi da masaniyar abun da zai faru da ke ɓoye in ba sanar da shi a ka yi ba. Haka nan ya fi ma alheri da Allah Maɗaukakin Sarki ya ɓoye ma na rana ko lokacin da za a karvi ran…
Read More
Game da kuskuren da sojoji suka yi kan masu Mauludi

Game da kuskuren da sojoji suka yi kan masu Mauludi

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ba tun yanzu ba ake samun matsaloli na kuskuren aiki da sojoji ke yi yayin hare-haren da suke kai wa kan ’yan ta'adda a wurare daban-daban na arewacin ƙasar nan, abin da ke haifar da asarar ɗimbin rayukan waɗanda ba su ji ba, ba su gani ba. Bincike ya nuna cewa, a dalilin irin wannan kuskure da sojoji ke yi an rasa rayukan ’yan Nijeriya aƙalla 425 tsakanin yara aanana, mata da maza, a lokuta daban-daban, daga shekarar 2017 zuwa 2023. Wani rahoto da ke bayyana sakamakon binciken da wata ƙungiya mai suna SBM Intelligence…
Read More
Kashi 70 na ma’aikatan kamfanin Mamuda ‘yan Kano ne – Gaddafi

Kashi 70 na ma’aikatan kamfanin Mamuda ‘yan Kano ne – Gaddafi

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Gaddafi Isyaku Hassan, jami'in cinikayya na kamfanin Mamuda, ya ce suna bada gudunmuwa ga mata domin ƙara musu ƙwarin gwiwa wajen sana'ar dogaro da kai, tarbiyya a zamantakewarsu na rayuwar aure a tarukansu daban-daban. Ya bayyana hakan ne ga manema labarai a wani taro da wasu mata suka gudanar da kamfanin ya bajekolin kayyakinsa da makarantu don qara musu ƙwarin gwiwa. Jami'in ya ce irin gudummuwar da suke bayarwa bai tsaya ga cigaban mata kaɗai ba har da ɓangaren ilimi har sai da ma'aikatar ilimi ta jihar Kano ta karramasu bisa irin jajircewa da  taimako…
Read More
Gwamnan Katsina ya bada umarnin dakatar da malami bisa zargin lalata da ɗalibarsa

Gwamnan Katsina ya bada umarnin dakatar da malami bisa zargin lalata da ɗalibarsa

Daga UMAR GARBA a Katsina Gwamnan jihar Katsina Umar Dikko Raɗɗa, ya bayar da umarnin dakatar da wani shugaban makarantar sakandare ta gwamnati da ke garin Ɗantankari a ƙaramar hukumar Ɗandume, bisa zarginsa da neman ɗalibarsa da lalata. Bayanin haka na ƙunshe cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai na ofishin sakataren gwamnatin jihar Abdullahi Aliyu 'Yar'adua ya saka wa hannu. A cewar sanarwar "Mai girma Gwamna ya karvi rahoton dake nuni da cewa ana zargin wani Lawal Ibrahim akan cin zarafin wata ɗaliba ta hanyar nemanta da lalata wanda shugaban makarantar sakandaren Ɗantankari ne dake ƙaramar hukumar Ɗandume. "Saboda…
Read More