20
Nov
Assalamu alaikum, Manhaja. Barkan ku da aiki, muna muku fatan Allah ya ƙara muku ƙwazo, Ameen. Ina kuma muku addu’a Allah ya ƙara muku hikima da basirar aiki da kuma bunƙasa wannan jarida mai farin jini baki ɗaya. A Arewa ne za ka samu gidan Almajirai da yara ba adadi, a Arewa ne za ka samu iyaye sun sake yaran su ana kwashewa ana sauya musu addini, a Arewa ne za ka samu gidan kangararru inda ake tara ɗaruruwan yara wai da sunan sun gagari iyayensu. Kwanaki kaɗan da suka wuce wata baiwar Allah ta saka wani bidiyo a shafin…