22
Feb
Daga FATUHU MUSTAPH Gwamnan jihar, Abubakar Sani Bello, ya karɓi mutum 53 da aka yi garkuwa da su kwanan baya a motar sufuri mallakar gwamnatin Neja (NSTA). Gwamnan ya karɓe su ne a fadar gwamnatin jihar da ke Minna, babban birnin jihar bayan da aka samu nasarar kuɓutar da su daga hannun ‘yan bindigar da suka kwashe su. Bello ya bayyana cewa, an yi nasarar kuɓutar da mutanen ne biyo bayan tattaunawa da dama da aka yi da kuma ƙwazon da gwamnati ta nuna. Yana mai cewa an kammala dukkan shirye-shirye don binciken lafiyar mutanen kafin a sada su da…
