Editor

9513 Posts
Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda da dama a Zamfara

Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda da dama a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD, a Gusau Dakarun rundunar haɗin guiwa ta arewa maso yammacin Najeriya Operation Hadarin Daji (OPHD) sun daƙile harin da 'yan ta'adda suka kai kauyen Danjibga dake ƙaramar hukumar Tsafe tare da daƙile ɓarnar amfanin gona a ƙauyen Faru dake ƙaramar hukumar Maradun duk a jihar Zamfara inda suka samu nasarar Kashe wasu da dama a batakashin da suka yi. Sojojin sun ce a yayin arangamar da ‘yan ta’addan sun samu nasarar hallaka guda uku daga cikin 'yan ta'addan, an kuma ƙwato bindigogi kirar AK-47 guda 3, kwanson alburusai 3, da kuma babura biyu. "A ranar 7 ga…
Read More
Amurka da Saudiyya sun gaza kawo ƙarshen rikicin Sudan

Amurka da Saudiyya sun gaza kawo ƙarshen rikicin Sudan

An gaza samar da cigaba a tattaunawar kawo ƙarshen rikicin Sudan da Saudiyya da Amurka suka kasance masu shiga tsakani, yayin da rashin jituwa tsakanin manyan hafsoshin sojin ƙasar biyu ta haifar da ƙalubale ga ayyukan jin ƙai a ƙasar. Rashin cigaba a tattaunawar da ke faruwa a birnin Jedda, ya rushe fatan da mutum sama da miliyan shida da rabi a ciki da wajen ƙasar ke yi, abin da ya ƙara haifar da taɓarɓarewar tattalin arziki da kuma rikicin ƙabilanci a Darfur. Yayin da rundunar sojin Sudan ɗin ta ce, ta ƙwace ikon babban birnin ƙasar, Khartoum, dakarun kai…
Read More
2023 AFCON: Dole ne Super Eagles su saka tunanin cin nasara – Aghahowa

2023 AFCON: Dole ne Super Eagles su saka tunanin cin nasara – Aghahowa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon ɗan wasan Nijeriya, Julius Aghahowa ya buƙaci Super Eagles da su bunƙasa tunanin samun nasara a gasar kofin Afrika na 2023. A rukunin A da Cote d'Ivoire, Equatorial Guinea da Guinea-Bissau, zakarun na AFCON sau uku za su sake lashe gasar karo na huɗu. Super Eagles za ta buxe gasar ta ne a AFCON 2023 da Equatorial Guinea a filin wasa na Alhassan Quattara, Ebimpe ranar 14 ga watan Janairu. Sai dai a wata hira da Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), Aghahowa ya bayyana cewa dole ne 'yan wasan su nuna jajircewa da juriya idan…
Read More
Mun shirya taron mata ne don ƙarfafa musu gwiwa kan sana’o’i – Stephanie Obia

Mun shirya taron mata ne don ƙarfafa musu gwiwa kan sana’o’i – Stephanie Obia

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano A ranar Asabar ɗin makon da ya gabata ne Zauren Mata da aka fi sani da "Mata Annual Conference" suka gudanar da taronsu na shekara a jihar Kano. Taron wanda ya samu halartar mata da kamfanoni daga ciki da wajen jihar Kano inda aka gudanar da jawabai na ƙarfafa gwiwar mata akan sana'o'i na dogaro da kai da kuma kyautata zamantakewa da mazajensu. Da take jawabi akan maƙasudin taron ɗaya daga cikin jami'ar da suka shirya taron, Stephnie Obia wacce 'yar ƙabilar Ibo ce haifaffiyar jihar Kano ta ce wannan shi ne taro karo na…
Read More
Masu buƙata ta musamman sun koka kan rashin wakilcinsu a gwamnatin Katsina

Masu buƙata ta musamman sun koka kan rashin wakilcinsu a gwamnatin Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Masu buƙata ta musamman a jihar katsina sun koka akan rashin wakilcinsu a majalisar zartaswa na gwamnatin Gwamna Dikko Umar Raɗɗa.            Hakan na faruwa ne duk da cewa an aiwatar da doka da ta bada kulawa na musamman a Nijeriya a lokacin gwamnatin Muhammadu Buhari da ta wuce.                              Shugaban ƙungiyar masu buƙata na musamman reshen jihar, Nasiru Dauda 'Yansiliyau ya faɗa wa manema labarai haka da yake magana akan ranar masa buƙata ta duniya.       …
Read More
Gaskiyar zance kan zargin da sojojin juyin mulkin Nijar ke yi wa Ambasada Tuggar

Gaskiyar zance kan zargin da sojojin juyin mulkin Nijar ke yi wa Ambasada Tuggar

*Sojoji da al'ummar Nijar ne matsalar ƙasar Daga BASHIR ALYU A tsakanin 'yan makonnin da suka gabata an yi ta yaɗa farfaganda a soshiyal midiya a Jamhuriyar Nijar inda ake zargin Ministan Harkokin Wajen Nijeriya kuma Shugaban Kwamitin Nazari da Tatutuwa Sha'anin Tsaro na ECOWAS, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar, na aiki da ra'ayin ƙasashen yamma musamman Faransa, wajen neman kuɓutar da Shugaba Bazoum da kuma ayyana lokacin da sojojin juyin mulki za su miƙa ragamar mulkin ƙasar. Juyin mulkin da ya auku a Nijar abu ne da ba za a lamunci aukuwarsa ba a ko'ina, kuma Nijeriya na da nauyin…
Read More
An yanke hukuncin kisa ga sojan da ya kashe Sheikh Goni Aisami

An yanke hukuncin kisa ga sojan da ya kashe Sheikh Goni Aisami

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kotu ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga sojan da ya kashe fitaccen malamin Musulunci a Jihar Yobe, Sheikh Goni Aisami. Babbar Kotun Jihar Yobe da ke zama a garin Potiskum, ta yanke wa korarren sojan, Las Kofur John Gabriel hukuncin rataya ne a ranar Talata. Alƙalin kotun, Usman Zanna Mohammed, ya kuma yanke wa abokin lafinsa, Las Kofur Adamu Gideon, hukuncin ɗaurin shekara 10 a gidan yari. Mai shari’a Usman Zanna Mohammed ya yanke wa Gabriel hukuncin ne ƙarƙashin dokar soja. Sojan da za a rataye yana aiki ne da bataliya ta…
Read More
’Yan bindiga sun wawashe takardun kotun zaɓen gwamnan Kogi

’Yan bindiga sun wawashe takardun kotun zaɓen gwamnan Kogi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wasu 'yan bindiga sun kai hari kan magatakardan Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓen gwamnan Jihar Kogi, David Umar Mike, tare da kwashe takardun masu ƙara. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar (PPRO), SP William Aya, ya bayyana hakan a Lokoja ranar Laraba. Hukumomin 'yan sandan sun ce maharan da suka kai harin na sakatariyar kotun sauraron ƙararrakin zaɓen gwamnan jihar sun kwashe dukkanin takardun ƙarar da wasu jam’iyyun siyasa biyar suka shigar. A cewar hukumomin ’yan sanda, takardun da aka kwace daga hannun Mike sun haɗa da, ƙorafe-ƙorafen da jam’iyyu huɗu (4): Action Alliance…
Read More
Gwamnatin Zamfara ta ƙwato motoci 50 daga hannun Matawalle

Gwamnatin Zamfara ta ƙwato motoci 50 daga hannun Matawalle

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Jihar Zamfara ta ce, ta kwato motoci kusan 50 mallakin gwamnatin jiha da ake zargin tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle ya tafi da su. Da yake zantawa da manema labarai ranar Alhamis a Gusau, Sani Sambo, mai magana da yawun gwamna Dauda Lawal ya ce matakin ya biyo bayan hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke Sokoto ta yanke a ranar Juma’ar da ta gabata. Ya qara da cewa, an bi tsarin da ya dace domin kwato motocin daga gidajen Gusau da Maradun na tsohon gwamnan wanda a baya ya musanta cewa ya mallaki…
Read More
Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya 9,000 daga 13,000 sun faɗi jarrabawar ƙarin girma

Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya 9,000 daga 13,000 sun faɗi jarrabawar ƙarin girma

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Aƙalla ma’aikatan gwamnati 9,000 da suka zana jarrabawar ƙarin girman ma’aikatan Gwamnatin Tarayya na shekarar 2022 sun faɗi. An samu wannan adadi ne daga Hukumar Ɗa’ar Ma’aikata ta Tarayya.An ce aƙalla ma’aikatan gwamnati 13,000 ne suka zana jarrabawar ta shekarar 2022, wadda aka gudanar a kusan cibiyoyin gwajin kwamfuta 69. An zaɓo ma'aikatan ne daga manyan ma’aikatan gwamnati, ’yan sandan Nijeriya, da sauran jami’an soji da sauran hukumomin tsaro. Wasiƙar mai ɗauke da jerin sunayen ma’aikatan da suka yi nasara ta kasance a ranar 30 ga Nuwamba, 2023 kuma an aiko ta daga Hukumar Kula da…
Read More