Editor

9438 Posts
Yadda mutuwar Daraktan Kannywood, Aminu S.Bono ta girgiza al’umma 

Yadda mutuwar Daraktan Kannywood, Aminu S.Bono ta girgiza al’umma 

*Gwamnan Kano ya girgiza da mutuwar Aminu S. Bono, inji Abba El-Mustapha*Rasuwar Bono ta haifar da wagegen giɓi a Kannywood – Ganduje*Zan biya ma sa bashin da ke kansa, cewar jaruma Aisha Humaira*Jaruma Rashida Maisa’a ta ɗauki nauyin karatun ɗan marigayin*Furodusa Kufaina ya yafe bashin da yake bin Bono Daga AISHA ASAS  Duk da cewa, mutuwa rigar kowa ce kuma mun amince duk mai rai sai ya ɗanɗani zafin mutuwa, hakan bai hana mu alhini da jimami yayin da muka rasa wani masoyinmu ba. Duk da kasancewar mutuwa abar tayar da hankali ce a kodayaushe, kuma babu ta yadda za…
Read More
Wane ne Adolf Hitler?

Wane ne Adolf Hitler?

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An haifi Adolf Hitler ranar 20 ga watan Afirilu na shekara 1889, ya kashe kansa ranar 30 ga watan Afirilu na shekara 1945 bayan an ci Jamus da yaƙi. An aifi Adolf Hitler ranar 20 ga watan Afrilu na shekara 1889 wato shekaru 122 kenan da suka gabata. An aife shi a wani gari mai suna Braunau-am Inn, a ƙasar Austriya kusa da iyakar ƙasar da Jamus. Shi ne na huɗu a gidansu. Mahaifinsa wani jami'in Custum ne, ya rasu a yayin da Hitler ke da shekaru 14 da aihuwa. Marubuta tarihin Hilter sun ce bai…
Read More
NARTO suna ƙoƙarin wajen wayar da kan direbobi – Muhammad Inuwa

NARTO suna ƙoƙarin wajen wayar da kan direbobi – Muhammad Inuwa

Daga MUHAMMADU MUJITTABA a Kano Alhaji Muhammad Inuwa Sakataren Ƙungiyar Masu Motocin Sufuri na Ƙasa, rashen Jihar Kano ya bayyana cewa, ƙungiyar su ta NARTO na taka muhimmiyar rawa wajen ganin ma'aikatan su sun bi duk kanin ƙa'idojin tuqi da kuma kula da lafiyar ababan hawan su a koda yaushe domin ganin an rage munanan haɗurran da akan samu akan hanyoyinmu na Nijiriya musamman a watanni huɗu ƙarshen kowacce Shekara. Kamar dai yadda sakataren ƙungiyar NARTO na Kano ya bayyana a lokacin taron wata ƙungiya mai suna MAMA da ta shirya don wayar da kan masu tuƙa ababan hawa da…
Read More
Gwamnan Kano ya naɗa sabon Shugaban Ma’aikatan Jihar

Gwamnan Kano ya naɗa sabon Shugaban Ma’aikatan Jihar

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin Alhaji Abdullahi Musa a matsayin sabon Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar. Hakan dai na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labaran Gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya aiko wa Manhaja, Inda ya ce naɗin na zuwa ne bayan da tsohon shugaban ma’aikatan jihar Kano, Usman Bala ya kammala aikinsa, inda ya yi ritaya daga aikin gwamnati tun a watan Mayun shekara ta 2023, kamar yadda doka ta tanada . Sanarwar ta ce Alhaji Abdullahi Musa ƙwararen ma’aikacin gwamnati ne da…
Read More
Sai an tallafa wa ƙananan masana’antu idan ana son karya farashin shinkafar gida – Ambasada Ali

Sai an tallafa wa ƙananan masana’antu idan ana son karya farashin shinkafar gida – Ambasada Ali

Daga MUHAMMADU MUJITTABA a Kano Ambasada Alhaji Ali Idris Mai Unguwa Kura, Shugaban Ƙungiyar Masu Sarrafa Shinkafa, Sayarwa da Noma ta na Ƙaramar Hukumar Kura, kuma Shugaban Ƙungiyar Masu Ƙananan Masana'antu da Matsakaita na Sarrafa Shinkafa na Ƙasa, reshan Jihar Kano, ya bayyana cewa ƙorafi da koke-koke da ake yi na tsadar shinkafa, wannan ya samo asali ne daga ƙarancin masu sarafa ta. Alhaji Ali ya ƙara da cewa, "idan har ana son noma shinkafa ya bunƙasa cikin tsafta, ya kuma wadata, da babu tsakuwa ko ƙuƙus, a cikin ta cikin farashi mai sauƙi da rahusa, sai an tallafawa ƙanana…
Read More
Cece-kuce ba zai canja hukunce-hukuncenmu ba – Alƙalai

Cece-kuce ba zai canja hukunce-hukuncenmu ba – Alƙalai

Daga BASHIR ISAH Babban Alƙalin Najeriya (CJN), Mai Shari'a Olukayode Ariwoola, ya jaddada cewa cece-kucen da ake yi a ƙasa ba zai canja hukunce-hukuncensu kan shari'un siyasa ba. Kawo yanzu, hukunce-hukuncen da Kotun Ƙoli ta yanke kan batutuwan zaɓe, wanda hakan ya yi sanadiyar soke nasarar wasu gwamnoni da 'yan majalisu, ya haifar da zazzafar muhawara a tsakanin 'yan ƙasa musamman 'yan siyasa. Da yake jawabi a wajen buɗe zama na musamman na fannin shari'a na 2023/2024 da kuma rantsar da sabbin manyan lauyoyin Nijeriya su 58, Ariwoola ya buƙaci alƙalai da su yi tsayin daka game da ayyukansu. Ya…
Read More
Dandalin shawara: Iyayena sun kai ni gidan mai mata huɗu a matsayin baiwa da ya siya (3)

Dandalin shawara: Iyayena sun kai ni gidan mai mata huɗu a matsayin baiwa da ya siya (3)

(Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS TAMBAYA: Anti Aysha Asas ina yini, ya lamura? Don Allah kar ki ambaci sunana, ko garin da nake. Wallahi na matsu ne, shi ya sa zan fallasa wannan sirrin don Ina son na samu mafita, saboda yanzu kaina ya yi zafi kan lamarin, ban san inda zan fuskata ba. Ina da shekara sha uku, uwata da kawuna da mai unguwarmu da wanda uwata take zaune gida nai, tana taya matansa aiki, suka shirya da ni, muka taho cikin garin………….da kayana da komai nau. Muka taho gidan wani babban mutum da yake da…
Read More
2024: Babu abin da zai dakatar da ni daga takarar Gwamnan Edo – Shaibu

2024: Babu abin da zai dakatar da ni daga takarar Gwamnan Edo – Shaibu

Daga BASHIR ISAH Mataimakin Gwnan Jihar Edo, Philip Shaibu, ya bayyana aniyarsa ta neman shiga takarar gwamnan jihar ya zuwa 2024. Ya ce zai tsaya takarar ne a ƙarƙashin Jam'iyyar PDP, tare da cewa, babu abin da zai hana shi neman kujerar gwamnan jihar. Shaibu ya bayyana aniyyar tasa ce da safiyar ranar Litinin a cibiyar Biohop Kelly Centre da ke Benin City, babban jihar. Da yake yi wa dandazon masoyansa jawabi, Shaibu ya ce a matsayinsa na ɗan asalin jihar wanda kuma ya san ciwon al'ummar jihar, zai nemi shugabancin jihar ne don cigabanta da ma al'ummarta baki ɗaya.…
Read More
Shari’ar kotunan Nijeriya ta zama tufka da warwara – PDP

Shari’ar kotunan Nijeriya ta zama tufka da warwara – PDP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babbar jam'iyyar adawa ta PDP a Nijeriya, ta bayyana hukunce-hukuncen da kotunan ɗaukaka qara suka yi, inda suka ƙwace nasarar wasu gwamnoni a matsayin "karan-tsaye" ga dimokraɗiyya. Jam'iyyar adawar na zargin APC mai mulkin Nijeriya ne da "amfani da qarfin iko" wajen tanqwara hukuncin kotunan, zargin da APC ta musanta. "Shari'ar Nijeriya ta zama kamar rawar 'yan mata yanzu; idan an yi gaba, sai a koma baya," inji Mataimakin Sakataren PDP na Ƙasa, Ibrahim Abdullahi. Ya ce dalilan da mutanen nan ke gabatarwa suna kwace zaɓen nan, akasari batutuwan da suka shafi kafin zaɓe…
Read More
Muna maraba da kafa jam’iyyar haɗaka kamar yadda Atiku ya nema – NNPP

Muna maraba da kafa jam’iyyar haɗaka kamar yadda Atiku ya nema – NNPP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam'iyyar adawa ta NNPP a Nijeriya ta nuna aniyarta ta shiga jam'iyyar haɗaka da sauran jam'iyyun adawa kamar yadda Atiku Abubakar ya nema a makon da ya gabata. Ɗan takarar na jam'iyyar PDP a zaven shugaban Nijeriya na 2023, Atiku ya zargi APC da yunƙurin mayar da Nijeriya bin tsarin jam'iyya ɗaya sannan ya yi kira ga jam'iyyun adawa da su dunqule don yin waje da jam'iyyar mai mulki. Shugaban Riƙo na NNPP na Ƙasa, Abba Kawu Ali, ya faɗa a yau Talata yayin wani taron manema labarai cewa kiran na Atiku abin a…
Read More