08
Dec
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wasu ’yan ta'adda da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne sun afka wa al’ummar Gandu tare da yin garkuwa da wasu ɗalibai a Jami’ar Gwamnatin Tarayya da ke Lafia. Wani ɗalibin jami’ar da ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida wa manema labarai cewa 'yan bindigar sun zo ne da farko a yawansu da misalin ƙarfe 7:30 na yammacin ranar Laraba inda suka fara harbi a iska don tsoratar da mazauna yankin, amma daga baya sun fara harbi kan mai uwa da wabi, lura da cewa jami'an tsaro na tahowa sai suka tsere cikin daji domin…
