Editor

9513 Posts
Harin Tudun Biri: Matasa sun gudanar da zanga-zangar nuna ɓacin rai a Kaduna

Harin Tudun Biri: Matasa sun gudanar da zanga-zangar nuna ɓacin rai a Kaduna

Daga BASHIR ISAH Wasu mata a garin Zariya, Jihar Kaduna, sun gudanar da zanga-zangar lumana domin nuna ɓacin ransu dangane da harin soji da ya faɗa kan masu maulidi a ƙauyen Tudun Biri da ke Ƙaramar Hukumar Igabi a jihar. An ga masu zanga-zangar sun yi tattaki a cikin garin na Zaria ɗauke da kwalaye masu ɗauke da saƙonni daban-daban kamar; "Adalci ga Arewa", "Adalci ga Igabi" da sauransu. Sama da mutum 80 ne suka mutu sannan wasu da dama sun tagayyara sakamakon harin da sojoji suka jefa bom har sau biyu ta hanyar amfani da jirgin sama mara matuƙi…
Read More
Yadda za ku raya soyayya bayan aure (2)

Yadda za ku raya soyayya bayan aure (2)

Tare da AMINA YUSUF ALI Masu karatu barka da wannan lokaci. Ina ƙara godiya ga waɗanda suka kira ni a waya da waɗanda suka yi tattaki suka zo don yi min ta'aziyya da taya ni jimamin rasuwar mahaifina Sheikh Dakta Yusuf Ali. Allah ya jaddada masa rahama ku kuma Allah ya bar zumunci da qauna kuma ya saka muku da alkhairi. A makon da ya gabata mun fara tattaunawa a kan yadda soyayya take mutuwa bayan aure da kuma dalilan da suke sakawa hakan ta faru. Sau da dama za ka ga an yi auren soyayya sosai amma sai ka…
Read More
Bakwai cikin 10 na matasan Nijeriya na harkar ‘Yahoo Yahoo’ – EFCC

Bakwai cikin 10 na matasan Nijeriya na harkar ‘Yahoo Yahoo’ – EFCC

Daga BASHIR ISAH Shugaban Hukumar Yaƙi da Rashawa (EFCC), Ola Olukoyede, ya ce abin damuwa ne matuƙa yadda ake samun da yawan matasan Nijeriya na shiga harkar damfara a intanet. Olukoyede ya bayyana a cikin wata sanarwa da EFCC ta wallafa a shafinta na X cewa, wannan bala'in ya kai matsayin da a yau, a cikin kowane 10 na ɗaliban Nijeriya za a tarar da 7 daga ciki suna ta'ammali da harkar damfara ta intanet. Ya nuna damuwarsa kan wannan batu ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar kamfanin Daar Communication PLC da suka kai ziyarar aiki a ofishinsa…
Read More
Me ke sa majinyatan ’yan fim ke ƙarewa da neman taimako? (1)

Me ke sa majinyatan ’yan fim ke ƙarewa da neman taimako? (1)

Daga AISHA ASAS  Tsayin shekaru ya zama wata al'ada a tsakanin masu nishaɗantarwa, musamman tsofaffin jarumai da suka samu shuhura a masana'antar finafinai ta Kudu, wato Nollywood na samun kansu a mawuyacin halin daga ƙarshe, har ya kai su ga neman taimako daga al'umma, ya Allah ko a sanadin ciwo, ko kuma talauci da ya yi masu katutu. Kaso mai yawa na jarumai da suka amsa sunansu ta ɓangaren nishaɗantar da masu kallonsu, suka samu karɓuwa, daga ƙarshe sun yi kira ga al'umma da su kawo masu ɗauki, ko dai ta ɓangaren rashin lafiya da ke buƙatar kuɗin magani, ko…
Read More
Harin Tudun Biri: Adadin waɗanda suka mutu ya kai 126

Harin Tudun Biri: Adadin waɗanda suka mutu ya kai 126

*Sau biyu sojoji na jefa mana bom, in ji wasu da suka tsira Daga BASHIR ISAH Kawo yanzu, adadin waɗanda suka mutu a harin kuskuren da sojoji suka kai Tudun Biri, cikin Ƙaramar Hukumar Igabi, Jihar Kaduna, ya kai 126. An tabbatar da hakan ne a lokacin da jami'an ƙungiyar Amnesty International suka ziyarci waɗanda harin ya shafa a ranar Talata. Wasu da suka tsira daga harin sun bayyana cewa, sau biyu sojojin na jefa musu bom. A ranar Lahadin da ta gabata wani harin bom da sujoji suka yi nufin kaiwa a kan 'yan ta'adda ya kuskure ya faɗa…
Read More
Tsakanin Hisba da Hukumar Tace Finafinai: Ko tafiya tare zai kai su ga nasara?

Tsakanin Hisba da Hukumar Tace Finafinai: Ko tafiya tare zai kai su ga nasara?

Daga AISHA ASAS  A kwanaki biyu baya, Hukumar Hisbah ta sasanta da masana’antar Kannywood, inda ta kai ga matsayar da za ta kawo zaman lafiya a tsakaninsu.  Hukumar Hisbah ƙarƙashin jagorancin shehin malami, Malam Aminu Ibrahim Daurawa, ta ce, ba za ta ƙara tunkarar masu shirya finafinai kai tsaye ba kan wani abu na rashin dacewa da suka aikata, maimakon haka za ta waiwayi Hukumar Tace Finafinai wadda ita ce ke da alhakin kula da lamarin da ya shafi wannan ɓangaren.  Hakan ya biyo bayan wani zama na musamman da hukumomin biyu suka yi tare da jagororin masana’antar Kannywood a…
Read More
Ministan Labarai zai shugabanci taron SAEMA/SCA na 2023

Ministan Labarai zai shugabanci taron SAEMA/SCA na 2023

Daga BASHIR ISAH Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai shi ne zai shugabanci taron SAEMA karo na biyar da za a yi haɗe taron SCA karo na uku wanda zai gudana ranar Alhamis, 7 ga Disamban 2023. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar taron da aka yaɗa. Sauran manyan jami'an da za su haskaka taron kamar yadda sanarwar ta nuna, sun haɗa da: Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Saha'anin Tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribadu; Shugaban NIPR, Dr. Ikeliaku; Babban Daraktan NITDA, Malam Kashifu Inuwa Abdullahi da dai sauransu. Taron wanda zai tattauna rawar da sadarwa ke…
Read More
Ko kun san daga ina ilimin lissafi ya samo asali?

Ko kun san daga ina ilimin lissafi ya samo asali?

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Duk da cewa babu wanda ya san asalin inda ilimin lissafi ya samo asali, amma a yau Blueprint Manhaja za ta yi duba ne kai tsaye zuwa ga ilimin lissafi, duk da cewa babu wani abu da ya rage game da daɗaɗɗen wajen tarihin lissafi da aka lalata a ƙarni na 13, amma mun binciko tare tattaro bayanan masana dangane da inda wajen yake da kuma yadda wajen yake. Sanin asalin ilimin lissafi abu ne mai wahalar gaske amma an fara ganin lissafai masu wahala ne a kusan shekara ta 3000 kafin bayyanar Annabi Isa (300…
Read More
Kisan mummuƙe ake yi wa Arewa

Kisan mummuƙe ake yi wa Arewa

Daga NAFI'U SALISU Sannu a hankali munanan abubuwa suna ƙara wanzuwa a Arewacin Nijeriya, irin abubuwan da suke da alaƙa da ɗaiɗaita ci gaban ƙasa, ko yankin ƙasa tare da alummar da suke rayuwa a cikin wannan wurin. An daɗe ana shirye-shiryen yadda za a rusa Arewacin Nijeriya, ta yadda za a maida ita tamkar Kufai (garin da ya tashi ya zam kango babu kowa a cikinsa). A cikin manyan Malamanmu na addinin Islama, Dakta Bin Usman ya taɓa yin wata lakca da a cikinta ya yi bayani na aƙalla awa da mintina 15, inda ya bayyana wasu abubuwa na…
Read More
Dubai: Mutum 422 aka ɗauki nauyinsu zuwa taron COP-28 – Malagi

Dubai: Mutum 422 aka ɗauki nauyinsu zuwa taron COP-28 – Malagi

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta maida martani kan ce-ce-ku-cen da ke yi game da adadin mutanen da ta ɗauki nauyi zuwa babba taron COP-28 da ke gudana a Dubai. Rahotanni sun ce tawagar Nijeriya na ɗaya daga cikin tawagogin da suka fi yawan mambobi da suka halarci taron wadda ke ƙunshe da mutum sama da 1000. Sai dai a ƙarin hasken da ya yi game da wannan batu, Ministan Labarai da Wayar da da Kan 'Yan Ƙasa, Mohammed Idris Malagi, ya ce, "Mutum 422 ne Gwamnatin Tarayya ta ɗauki nauyinsu zuwa wurin taron", amma ba sama da 1000 kamar…
Read More