Editor

9513 Posts
‘Yan kasuwa sun buƙaci a ɗaga farashin fetur

‘Yan kasuwa sun buƙaci a ɗaga farashin fetur

Daga AISHA ASAS 'Yan kasuwar man fetur sun ce bisa la'akari da yadda abubuwa ke tafiya a kasuwar ɗanyen mai ta duniya, kamata ya yi farashin fetur kan lita guda ya zama tsakanin N185 zuwa N200 a Nijeriya. Bayanan da Manhaja ta kalato sun nuna an samu tashin farashin fetur a kasuwar mai ta duniya a makon da ya gabata wanda hakan ya sanya 'yan kasuwar nuna damuwarsu kan yadda ba a aiwatar da cikakken shirin sakar wa 'yan kasuwar mara ba a harkar man fetur, lamarin da ya hana samun sauyin farashin litar fetur sama da watanni biyu A…
Read More
Babu abin da zai cika sai da mace a ciki – Hajiya Halima

Babu abin da zai cika sai da mace a ciki – Hajiya Halima

Hajiya Halima Idris ita ce Mai Taimaka wa Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmed El-Rufa’i, a fannin Fikira da Ƙirƙira. Ta yi fice ta fuskoki da dama tun gabanin muƙamin ta, musamman wajen kishin Arewa da son cigaban mata da matasa. A wannan hirar da wakiliyar manhaja, AISAH ASAS, ta  yi da Halima Idris, ta bayyana abubuwa da dama da suka haɗa da ayyukan ta  a gwamnati da kuma fannin kwalliya. Ga yadda hirar ta kasance: Kin yi fice a harkokin cigaban matasa da suka shafi fikira da ƙirƙira. Me ya ba ki wannan sha’awar?Gaskiya ba zan iya ce miki…
Read More
Rikicin addini: Salafiyya, Tijjaniya da Ƙadiriyya 

Rikicin addini: Salafiyya, Tijjaniya da Ƙadiriyya 

Daga FATUHU MUSTAPHAA cikin makon da ya gabata ne, wasu manyan malaman salafiya, waɗanda suka haɗa da: sheikh Muhammad bin Abdulwahab da Sheikh Dr Mansur Sokkoto, suka yi kira ga gwamnatin jihar Kano da ta kama shehin malamin nan na ɗarikar Ƙadiriya: Sheikh AbdulJabbar Nasiru Kabara. Wannan rigima dai ta samo asali ne, tun bayan da shi Sheikh Abduljabbar ya fara wani tafsiri da ya kira Jauful Faraa. Tafsirin da mafiya akasarin malaman ɗarikar ta Salafiya ke ganin ya saɓa ƙa’ida, ya na kuma wuce gona da iri. Wannan rigingimu dai ba yau aka fara fama da su, a tarihin…
Read More
Babban buri na kafin in bar duniya…, inji Bilkisu

Babban buri na kafin in bar duniya…, inji Bilkisu

Daga AISHA ASAS Waɗanda suka daɗe da fara karance-karancen littattafan Adabin Kasuwar Kano tun wuraren 1993 ba shakka zan iya cewa sun sha cin karo da littattafan Hajiya Bilkisu Salisu Ahmed Funtua, wadda ake kira Aunty Bilki Funtua, domin ta kasance a sahun farko kuma tauraruwar da littattafanta ke ja a wancan lokacin. Saboda haka a tashin farko muka samu nasarar shigo muku da ita cikin wannan fili don jin wace ce ita, mene ne kuma burinta a halin yanzu sakamakon rashin jin duriyar littattafan ta a kasuwa na dogon lokaci. Ga dai yadda hirar tamu ta kasance: Masu karatu…
Read More
Ambaliya: Ɗan Majalisa ya shige wa mazaɓarsa gaba wajen samun tallafi

Ambaliya: Ɗan Majalisa ya shige wa mazaɓarsa gaba wajen samun tallafi

Daga WAKILIN MU Ɗan Majalisar Wakilai ta Ƙasa Hon. Nicholas Ossai na jam'iyyar PDP daga jihar Delta, ya yi sanadin rabon tallafin kayayyaki da dama da kuɗinsu ya kai Naira miliyan 30 ga jama'ar da ambaliya ta shafa gundumar Ndokwa/Ukwuani da ke jihar. Hon. Ossai ya ce Hukumar Bada Gajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ce ta bada tallafin da aka rabar wa waɗanda lamarin ya shafa. A bayanin da ya yi Lahadin da ta gabata, ɗan majalisar ya ce kayayyakin tallafin da aka rabar sun haɗa da kwanon rufi, ƙusoshi, silin, siminti, katifu, hidan sauro, barguna, kayan abinci da dai…
Read More
Legas: NAFDAC ta rufe kamfani mai sayar da kayayyakin da wa’adin amfaninsu ya ƙare

Legas: NAFDAC ta rufe kamfani mai sayar da kayayyakin da wa’adin amfaninsu ya ƙare

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC) ta rufe wani kamfanin sarrafa abinci a Jihar Legas bisa laifin sayar wa jama'a da sinadarin haɗa abinci (Thyme da Curry) bayan kuma wa'adin amfaninsu ya ƙare. NAFDAC ta ce ta ɗauki wannan mataki ne domin tsaftace Nijeriya daga abinci mara inganci domin ci gaba da kare lafiyar 'yan ƙasa. A sanarwar da jami'in yaɗa labarai na shiyya na hukumar Sayo Akintola ya fitar, Babbar Daraktar hukumar Prof. Mojisola Adeyeye ta bayyana damuwarta kan lamarin. Tana mai cewa za a ƙaƙaba wa kamfanin da lamarin ya…
Read More
Afirka ta Kudu ta fasa shirin yi wa ‘yan ƙasar rigakafin korona

Afirka ta Kudu ta fasa shirin yi wa ‘yan ƙasar rigakafin korona

Daga AISHA ASAS Ƙasar Afirka ta Kudu ta ce ta fasa shirin yi wa 'yan ƙasar allurar rigakafin cutar korona da ta so somawa bayan da ta gano cewa gwajin maganin AstraZeneca jab da ta yi ya kasa yaƙar nau'in cutar da ya bayyana a ƙasar. Afirka ta Kudu ita ce ƙasar da ta fi kowace ƙasa harbuwa da cutar a faɗin nahiyar Afirka, inda ta so soma aiwatar da shirin yi wa 'yan ƙasar allurar rigakafin korona da ta mallaka daga AstraZeneca da Oxford. A cewar Ministan Lafiyar ƙasar Zweli Mkhize, "Mun dakatar da rigakafin na wucin-gadi har sai…
Read More
Cutar Korona: Abu Dhabi ta haramta tarurrukan shaƙatawa da na bukukuwa

Cutar Korona: Abu Dhabi ta haramta tarurrukan shaƙatawa da na bukukuwa

Daga BASHIR ISAH A matsayin wani mataki na yaƙi da yaɗuwar annobar korona a Abu Dhabi, Kwamitin Kula da Agajin Gaggawa, rikice-rikice da Ibtila'i na Abu Dhabi ya sanya dokar haramta tarurrukan shaƙawata da na bukukuwa a faɗin birnin sai dai ɗan abin da ba za a rasa ba. Kwamitin ya ce daga ranar 7 ga Fabrairun 2021, an taƙaita adadin mutane da aka amince su halarci taron bikin aure da na zumunta zuwa mutum 10, sannan mutum 20 game da tarurrukan da suka shafi jana'iza da zaman makoke. Haka nan an taƙaita yawan mutanen da aka yarda su gudanar…
Read More
2023: Ba za mu zaɓi matsafa ba a Akwai Ibom – Mbang

2023: Ba za mu zaɓi matsafa ba a Akwai Ibom – Mbang

Daga WAKILIN MU Tsohon Shugaban Ƙungiyar Kiristoci ta Ƙasa (CAN) Sunday Mbang, ya gargaɗi 'yan siyasar jihar Akwa Ibom masu neman tsayawa takara a zaɓuɓɓukan 2023 da su nesanta kansu da harkokin ƙungiyar asiri. Mbang ya yi wannan gargaɗi ne sa'ilin da yake amsa tambayoyin manema labarai a wajen taron addu'a ta musamman da aka shirya wa 'yan majalisun tarayya daga jihar don nema musu kariya daga cutar korona a ƙarshen mako a Uyo, babban birnin jihar. Jagoran addinin ya ce Allah ba zai bari duk wani ɗan siyasa a jihar mai mu'amala da tsafi da makamancin haka ya zama…
Read More
‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 4 a Tungan Maje

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 4 a Tungan Maje

Daga AISHA ASAS Wasu 'yan bindiga sun kai hari a Tungan Maje da ke yankin Gwagwalada, Abuja, inda suka yi garkuwa da wasu mutum huɗu. Al'amarin wanda ya auku a tsakar daren wannan Lahadin, sai da 'yan bindigar suka shafe kimanin sa'o'i uku suna abin da suka ga dama a Tungan Maje kafin daga bisani suka yi awon gaba da wani tsohon jami'in Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) Abdulahi Idris Rakieu da wasu mutum biyu daga iyalan gidansa. A cewar jaridar TheCable, harin ya shafi wani mai suna Olusola Agun, wanda shi ya zama cikon na…
Read More