Zaɓen Bayelsa, Imo, Kogi: Ban da nuna halin a-yi-rai-ko-a-mutu, kiran Kwamitin Abdulsalami ga ‘yan siyasa

Daga BASHIR ISAH

Shugaban Kwamitin Wanzar da Zaman Lafiya na Ƙasa, Janar Abubakar Abdulsalami (rtd), ya yi kira ga jam’yyun siyasa da magoya bayansu da a guji nuna halin a-yi-rai-ko-a-mutu yayin zaɓen gwamnonin da za a gudanar ranar Asabar a jihohin Bayelsa da Kogi da kuma Imo.

Abdulsalami ya yi wannan kira ne yayin da jam’iyyin siyasa su 18 da za su fafata a zaɓen gwamna a Jihar Kogi suka rattaɓa hannun kan yarjejeniyar zaman lafiya ranar Laraba a jihar.

Da yake jawabi ta bakin wakilinsa Cardinal John Onaiyekan, tsohon shugaban ƙasar ya ce: “Wannan taro na da muhimmanci saboda lamarin zaɓe a Nijeriya ya zama na a-yi-rai-ko-a-mutu wanda hakan ba alheri ba ne ga ƙasa da al’ummarta.”

Kazalika, Abdulsalami ya yi kira ga Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) da ta yi adalci a zaɓen da za a gudanar.

Ya ce zaɓuɓɓuka a Nijeriya za su gudana cikin lumana muddin masu ruwa da tsaki kowa ya sauke nauyin da ya rataya a wuyansa.

Ya ƙara da cewa, lokaci ya yi da ya kamata ‘yan takara su gabatar da kansu wajen jama’a don neman zaɓe maimakon ɗauki-ɗora tare da danne wa masu kaɗa ƙuri’a ‘yancin zaɓen wanda suke so.

A nasa ɓangaren, Bishop Mathew Hassan Kukah wanda ya samu wakilcin Attah Barkindo a wajen taron, ya buƙaci ‘yan siyasa kowa ya natsu domin a samu zaɓe ya gudana cikin ruwan sanyi.