Editor

9513 Posts
Biyan diyyar rusau: Gwamnatin Kano ta miƙa wuya

Biyan diyyar rusau: Gwamnatin Kano ta miƙa wuya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Jihar Kano a ƙarƙashin jagorancin Abba Kabir Yusuf ta miƙa wuya, inda amince za ta biya diyyar Naira Biliyan Uku ga ƙungiyar masu shagunan masallacin idi da ke birnin Kano, saboda rusa musu kadarorin da aka yi musu ba bisa ƙa’ida ba. An cimma yarjejeniyar ne ta wata takardar neman sasanci a ranar 12 ga Disamba tare da gabatar da ƙara a ranar 13 ga Disamba ta hannun lauyoyi a gaban Mai Shari’a Inyang Ekwo na Babbar Kotun Tarayya da ke AbujaKamfanin Dillancin Labaran Nijeriya ya bayyana hakan ne biyo bayan rushe shagunan…
Read More
NLC ta sa zare da gwamnati kan ƙin biyan ma’aikata N35,000 na cire tallafi

NLC ta sa zare da gwamnati kan ƙin biyan ma’aikata N35,000 na cire tallafi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙungiyar Ƙwadago (NLC da TUC) ta gargaɗi Gwamantin Tarayya kan ƙin biyan ma’aikata tallafin N35,000 da ta yi musu alƙawari duk wata kan cire tallafin mai. Ƙungiyar Ƙwadago ta yi gargaɗin ne a lokacin da take zargin Gwamnatin Tarayya da saɓa alƙawarin da ta yi na biyan ma’aikata N35,000 na tsawon wata shida domin rage raɗaɗin cire tallafin mai. Shugaban ƙungiar TUC, Festus Osifo bayyana cewa ma’aikata sun shaida musu cewa sau ɗaya kaɗai gwamnatin ta biya N35,000 daga lokacin da Shugaba Tinubu ya sanar da matakin. Ya ce savanin alƙawarin biyan kuɗin da…
Read More
Sarkin Ƙabilar Ibo na Kafanchan ya jinjina wa Sarkin Jama’a bisa haɓɓaka zaman lafiya

Sarkin Ƙabilar Ibo na Kafanchan ya jinjina wa Sarkin Jama’a bisa haɓɓaka zaman lafiya

Daga ABUBAKAR LABARAN a Kafanchan Sarkin Ƙabilar Ibo mazauna garin Kafanchan da kewaye, Maigirma Richard Ogbonna ya jinjina wa Mai Martaba Sarkin Jama'a Alhaji Muhammadu Isa Muhammadu saboda hovvasarsa dangane da harkokin da suka shafi jaddada zaman lafiya. Richard Ogbonna ya yi wannan jinjinan ne a saƙonsa na fatan alkhairi jim kaɗan bayan da aka kammala bukukuwan cika shekaru 25 a karagar mulki da sarkin ya gudanar a garin Kafanchan. Sarkin Ibon ya qara da cewa Sarkin Jama'a bai taɓa yin ƙasa a guiwa ba dangane da al'amurran da suka shafi zaman lafiya mai ɗorewa a ƙasarsa da kewaye. Ya…
Read More
Raɗɗa ya jagoranci jami’an tsaro wajen shiga daji don farautar ‘yan bindiga a Katsina

Raɗɗa ya jagoranci jami’an tsaro wajen shiga daji don farautar ‘yan bindiga a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Gwamna Dikko Umar Raɗɗa na jihar Katsina tare da ayarin jami'an tsaro sun shiga dajin Zakka domin farautar 'yan bindiga. An dai yi arangama da 'yan bindigan da jami'an tsaron inda jami'an tsaron suka samu nasarar kuɓutar da wani mutum ɗan shekara talatin da uku. Gwamnan ya je karamar hukumar Safana a bisa gayyatar mataimakin kakakin majalisar dokoki na jihar don ƙardamar da bada tallafin kayan abinci da mataimakin kakakin majalisar ya samar. Ana cikin bikin bada tallafin ne sai gwamnan ya samu labari shigowar 'yan bindigan garin Zakka inda nan take ya bi ayarin…
Read More
Shugabanci nagari ne hanyar samun ci gaban yankinmu – Tinubu

Shugabanci nagari ne hanyar samun ci gaban yankinmu – Tinubu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Nijeriya kuma Shugaban Ƙungiyar Ecowas, Bola Tinubu ya yi kira ga shugabannin ƙasashen Afirka ta Yamma da su fifita samar da shugabanci nagari ga mutanen yankin, saboda a cewarsa shi ne kawai hanyar inganta da ci gaban tattalin arzikin yankin. Yayin da yake gabatar da jawabi a wajen taron ƙungiyar da aka gudanar a birnin Abuja na Nijeriya, shugaba Tinubu ya ce tsarin shugabanci nagari ne zai magance tarin matsalolin da al'umomin ƙasashen yankin ke fama da su, kamar inganta rayuwa da samar da kyakkyawan yanayin samar da gaba mai ɗorewa. Shugaban na…
Read More
Abin da ya sa muka sadaukar da albashinmu ga mutanen Tudun Biri — Ndume

Abin da ya sa muka sadaukar da albashinmu ga mutanen Tudun Biri — Ndume

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja 'Yan Majalisar Dattawan Nijeriya 109 sun sanar da sadaukar da albashinsu na wata guda ga dangin mutanen da harin kuskuren da rundunar sojin Nijeriya ta kai garin Tudun Biri, da ke Ƙaramar Hukumar Igabi, a jihar Kaduna ya yi ajalinsu. 'Yan Majalisar sun ce za a yi amfani da kuɗin, da yawansu ya kai Naira miliyan 109, wato miliyan guda daga kowanne sanata domin hidimtawa mutanen, da zummar rage masu raɗaɗin halin da suke ciki. Sanata Ali Ndume, mai tsawatarwa a majalisar dattawan Nijeriyar, wanda kuma ke cikin 'yan Majalisar da suka ziyarci jihar…
Read More
Amurka da Birtaniya sun ƙara wa Hamas takunkumai

Amurka da Birtaniya sun ƙara wa Hamas takunkumai

Amurka da Birtaniya sun sanar da ƙara wa Hamas sabbin takunkumai sakamakon harin da ƙungiyar ta kai wa Isra'ila a ranar 7 ga watan Oktoban, inda aka samu salwantar rayuka. Ma'aikatar Baitul Malin Amurka ta ce, wannan matakin ya shafi manyan jami'an da ke ruruta manufar ta'addacin Hamas ta hanyar wakiltar manufofin ƙungiyar a ƙasashen ƙetare tare da kula da asusunta. Tun bayan harin na Oktoba da ƙungiyar ta ƙaddamar da ya kashe kimanin mutane dubu ɗaya da ɗari biyu, akasarinsu fararen hula, tare da garkuwa da mutane 240, Amurka ke matsin lamba kan mayaƙan. Baitul Mali Amurka ya ce,…
Read More
Osimhen da Oshoala: ’Yan Nijeriya da suka lashe kyautar gwarazan ‘yan wasan Afirka a 2023

Osimhen da Oshoala: ’Yan Nijeriya da suka lashe kyautar gwarazan ‘yan wasan Afirka a 2023

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan wasan tawagar Nijeriya, Victor Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan ƙwallon ƙafar Afirka na 2023, inda takwararsa, Asisat Oshoala a ɓangaren ƙwallon ƙafar mata ta zama gwarzuwar ’yar wasan ta Afirka. Ɗan wasan Super Eagles ya lashe kyautar a bikin da aka gudanar a Marrakech, wanda ya ja ragamar Napoli ta lashe Serie A karon farko bayan shekara 33. Osimhen ya yi takara tare da ɗan wasan Morocco Achraf Hakimi da na Masar Mohamed Salah. Ɗan wasan shi ne ya kai Super Eagles gasar kofin Afirka da za a yi a Ivory Coast a baɗi,…
Read More
Tsadar rayuwa: Ku ƙara haƙuri da lamarin Tinubu, roƙon Malagi ga ‘yan Nijeriya

Tsadar rayuwa: Ku ƙara haƙuri da lamarin Tinubu, roƙon Malagi ga ‘yan Nijeriya

Daga BASHIR ISAH Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan ‘Yan Ƙasa, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ya roƙi ‘yan Nijeriya da su ƙara haƙuri da lamarin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu dangane da sabbin tsare-taren da ta fitar da nufin daidaita tattalin arzikin ƙasa. Malagi ya yi wannan roƙo ne sa’ilin da yake jawabi a wajen taron ƙaddamar da littafi ranar Alhamis a Birnin Tarayya. Ministan ya yarda cewa lallai ‘yan Nijeriya na fuskantar tasku sakamakon sabbin tsare-tsaren gwamnati, yana mai ccewa gwamnatin na yin abin da take yi ne domin daidaita wa tattalin arzikin ƙasa zama yadda ya kamata.…
Read More
Nazari: Yadda Gasar Hikayata ta BBC Hausa ke ɗaukaka muryar mata 

Nazari: Yadda Gasar Hikayata ta BBC Hausa ke ɗaukaka muryar mata 

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU "Ta dalilin wannan gasa ta Hikayata da BBC Hausa suke shiryawa mata marubuta da a baya ba a san da su ba, yanzu sunan su ya fito. Tabbas gasar tana ɗaga muryar mata ta yadda za su isar da kukansu da bayar da shawarwari na hanyoyin inganta rayuwar mata da zamantakewar al'umma." Aisha Adam Hussaini kenan ƴar shekara 27 da ta fito daga Jihar Kano, wacce ta zama gwarzuwa ta ɗaya a Gasar Hikayata ta BBC Hausa ta 2023, yayin da take yabawa da yadda ake gudanar da gasar rubuta gajeren labari ta marubuta mata.  "Na…
Read More