Editor

9513 Posts
Ambasadar EU ta ziyarci jihar Nasarawa a karon farko

Ambasadar EU ta ziyarci jihar Nasarawa a karon farko

Daga JOHN D. WADA, a Lafiya Ambasadar Ƙasashen Yamma, wato European Union a Nijeriya, Samuela Isopi ta bayyana niyar ƙasashen yamman na haɗa kai da gwamnatin jihar Nasarawa a fannin bunƙasa tattalin arziki na zamani da noma da sauyin yanayi don cigaban jihar baki ɗaya. Ambasada Isopi ta bayyana haka ne a jawabin ta a lokacin da ta kai ziyarar aiki jihar Nasarawa inda ta gana da Gwamnan jihar Injiniya Abdullahi Sule a gidan gwamnati da ke Lafiya a cikin mako da ake ciki. Acewarta maƙasudin ziyarar ta shi ne don ƙarfafa dangantaka tsakanin EU da jihar Nasarawa da kuma…
Read More
Ɓarayin daji sun saki ɗaliban jami’ar Dutsinma bayan shafe fiye da wata biyu a tsare

Ɓarayin daji sun saki ɗaliban jami’ar Dutsinma bayan shafe fiye da wata biyu a tsare

Daga UMAR GARBA a Katsina Ɓarayin daji sun saki sauran ɗaliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Dutsinma a jihar Katsina, wato FUDMA, bayan shafe fiye da wata biyu a hannun ɓarayin. Shugaban makarantar, Farfesa Arma Ya'u Hamisu Bichi ne ya shaida wa BBC cewa ya samu labarin sakin ɗaliban daga ɗaya daga cikin mahaifan ɗaliban a yammacin ranar Asabar. Tun farko Blueprint Manhaja ta bayyana cewar, a ranar 4 ga watan Oktoba, wasu 'yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun kutsa kai a wani gida kusa da makarantar Mariamo Ajiri a ƙaramar hukumar Dutsinma inda ɗaliban ke haya suka kuma yi…
Read More
Za mu ɗage wa Nijar takunkumi idan sun so – ECOWAS

Za mu ɗage wa Nijar takunkumi idan sun so – ECOWAS

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mista Sidie Tunis, Shugaban Majalisar ECOWAS, ya ce za a ɗage takunkumin da aka ƙaƙaba wa Jamhuriyar Nijar, idan har gwamnatin soja ta saki Shugaba Mohamed Bazoum. Shugaban majalisar ya ba da wannan tabbacin ne a lokacin da tawagar mutane 19 daga ƙungiyar ‘yan Afrika suka kai masa ziyarar ban girma a Abuja. Ziyarar dai ita ce ta sanya majalisar ta goyi bayan ɗage takunkumin da aka ƙaƙaba wa Nijar domin rage raɗaɗin da talakawa ke fuskanta a ƙasar. Shugaban majalisar ya buƙaci tawagar da ta saki Bazoum da iyalansa ba tare da wani…
Read More
Kasafin kuɗin Ma’aikatar Tsaro na 2024 ya yi kaɗan – Badaru

Kasafin kuɗin Ma’aikatar Tsaro na 2024 ya yi kaɗan – Badaru

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan Harkokin Tsaro, Abubakar Badaru, ya roƙi Majalisar Tarayya su ƙara wa ma’aikatarsa kason kuɗaɗe cikin kasafin 2024. Ministan ya yi wannan roƙo ne a ranar Laraba, lokacin da ya bayyana a gaban Kwamitin Majalisar Dattawa da na Tarayya, a wani zaman tare da suka yi, a Majalisar Ƙasa, a Abuja. Badaru da bayar da dalilan da suka haɗa da tashin tsadar gudanar da ayyukan sojoji, ƙarin farashin dizal da fetur da sauran dalilai. Cikin kasafin 2024 dai an ware wa Ma’aikatar Tsaro Naira bilyan 78.5 domin biyan albashin sojoji da kuma gudanar da…
Read More
APC ta nemi gwamnan Zamfara ya zauna a jihar don fuskantar matsalar tsaro

APC ta nemi gwamnan Zamfara ya zauna a jihar don fuskantar matsalar tsaro

Daga SANUSI MUHAMAD a Gusau Jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara ta yi Allah-wadai da sake ɓarkewar ayyukan ‘yan bindiga a jihar wanda ya kai ga kashe-kashe da yin garkuwa da mutane da kuma raunata mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, daga hannun ‘yan ta’addan, inda ta dorawa Gwamna Dauda Lawal da ya dawo jihar domin daƙile zubar da jinin al’umma. Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da aka raba wa manema labarai mai ɗauke da sa hannun sakataren yaɗa labaran jam’iyyar na jihar Yusuf Idris a ranar Laraba. Sanarwar ta ƙara da cewa, “Hare-haren da…
Read More
Cibiyar Horti Nigeria ta tallafa wa mata manoma 2,000 a Kano da Kaduna

Cibiyar Horti Nigeria ta tallafa wa mata manoma 2,000 a Kano da Kaduna

Daga NASIR S. GWANGWAZO Cibiyar Horti Nijeriya wacce take samun kulawar IFDC da take samun tallafi daga ƙasar Neitherland, domin bunƙasa noman kayan lambu, musamman tumatur, albasa, kabeji da kokwanba, ta gudanar da wani taro na tallafa wa mata guda 2,000 a jihohin Kano da Kaduna, waɗanda suka fito daga ƙananan hukumomi daban-daban na jahohin. Cibiyar dai ta shiga ƙauyuka daban-daban, inda ta nemi ƙungiyoyi manoma mata kuma ta tallafa musu da yadda za su dogara da kansu, don samun bunƙasar arziki. Horti Najeriya ta tantance ƙungiyoyin da suka fi nuna ƙwazo a yayin da suka baje fasahohi daban-daban na…
Read More
Matar da ta hukunta ɗiyar kishiyarta da wuta za ta fuskanci hukunci – Gwamnatin Zamfara

Matar da ta hukunta ɗiyar kishiyarta da wuta za ta fuskanci hukunci – Gwamnatin Zamfara

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Jihar Zamfara ta ce za ta gurfanar da wata mata da ake zargi da laifin cin zarafin ɗiyar kishiyarta mai shekaru 12 a garin Tsafe da ke yankin ƙaramar hukumar Tsafe a jihar. Kwamishinar mata, yara da cigaban al’umma ta jihar ta Zamfara, Dr Nafisa Muhammad, ta bayyana hakan a lokacin da ta ziyarci wanda abin ya shafa. Kwamishinar ta ce, "mun samu rahoton cewa wata Aisha Mustapha da ke garin Tsafe ta yi wa ɗiyar kishiyarta ‘yar shekara 12 illa ta hanyar narka leda a jikinta tare da tilasta mata shan fitsari."…
Read More
Dambarwar Jihar Ribas: Kwamishinan Shari’a ya yi murabus

Dambarwar Jihar Ribas: Kwamishinan Shari’a ya yi murabus

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Yayin da rikicin siyasa ke daɗa ƙamari a Jihar Ribas, kwamishinan shari'a na jihar, Farfesa Zacchaeus Adangor ya murabus daga muƙaminsa. Sai dai a wasiqarsa ta ajiye aiki, Adangor ya faɗa wa Gwamna Similanayi Fubara cewa ya ɗauki matakin saboda wasu dalilai na ƙashin kai. Adangor wanda ya riqe muƙami a gwamnatin baya ta Nyesom Wike, ya yaba wa gwamna Fubara saboda ba shi damar yin aiki a ƙarƙashinsa. Ƙurar rikicin siyasa ta turnuƙe a jihar ta Rivers tun bayan da aka fara samun savani tsakanin tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike da gwamnan jihar Similanyi Fubara.…
Read More
Muna haɗa hannu da Majalisar Dokoki don inganta Nijeriya – Tinubu

Muna haɗa hannu da Majalisar Dokoki don inganta Nijeriya – Tinubu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce, ƙoƙarin da gwamnatinsa ke yi na sauya fasalin tattalin arzikin Nijeriya yana haifar da ɗa mai ido tare da goyon bayan Majalisar Dokoki ta Ƙasa ƙarƙashin jagorancin Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas. Da yake jawabi a wajen taron bikin cika shekaru 61 na Shugaban Majalisar Dattawa a ranar Alhamis a Abuja, shugaban ƙasar ya ce za a yi nazari kan ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta daga ɓangaren zartarwa da na majalisa da nufin samar da hanyoyin da za a iya aiwatar da su…
Read More
Kisan bom: Al’ummar Tudun Biri sun yi tutsun zuwa kotu

Kisan bom: Al’ummar Tudun Biri sun yi tutsun zuwa kotu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Al’ummar ƙauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna sun yi tutsu bisa ƙarar da aka shigar da sunansu a Babbar Kotun Tarayya Kaduna ta neman Gwamnatin Tarayya ta biya su diyyar Naira biliyan 33 kan kuskuren harin boma-bomai da aka kai, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 100 tare da jikkata wasu da dama. Dagacin ƙauyen Tudun Biri, Malam Balarabe Garba, ne ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar godiya ga Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, inda ya ce, sun samu labarin cewa, wasu sun garzaya kotu a madadinsu.…
Read More