18
Dec
Daga JOHN D. WADA, a Lafiya Ambasadar Ƙasashen Yamma, wato European Union a Nijeriya, Samuela Isopi ta bayyana niyar ƙasashen yamman na haɗa kai da gwamnatin jihar Nasarawa a fannin bunƙasa tattalin arziki na zamani da noma da sauyin yanayi don cigaban jihar baki ɗaya. Ambasada Isopi ta bayyana haka ne a jawabin ta a lokacin da ta kai ziyarar aiki jihar Nasarawa inda ta gana da Gwamnan jihar Injiniya Abdullahi Sule a gidan gwamnati da ke Lafiya a cikin mako da ake ciki. Acewarta maƙasudin ziyarar ta shi ne don ƙarfafa dangantaka tsakanin EU da jihar Nasarawa da kuma…
