Editor

9513 Posts
Saƙo ga Musulmai daga Tiktok

Saƙo ga Musulmai daga Tiktok

Na yi dogon rubutu na kammala a kan wannan bidiyo, amma sai na neme shi na rasa. Dole sai da na sake komawa tiktok na nemo bidiyo ɗin. Ina ganin wannan bidiyo na ƙasa yana ishara ne da hadisin da aka ce Manzon Allah (SallalLahu alaihi wa sallam) ya faxa ne, da yake cewa "…Dan Allah ku kula da mata". A fahimtata ya danka su amana ne a hannunmu, amma ko shakka babu, wannan amana ta mata da 'ya'ya da aka damqa mana, ta tabbata da yawa daga cikinmu mun ci wannan amana. Da farko dai, a jiya da dare…
Read More
Likitoci sun janye aniyarsu ta gudanar da zanga-zanga

Likitoci sun janye aniyarsu ta gudanar da zanga-zanga

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Likitoci ta Nijeriya (NARD) ta dakatar da shirinta na gudanar da zanga-zangar gama-gari don nuna wa gwamnati rashin jin daɗinta na rashin cim ma buƙatunta. NARD ta janye aniyar tata ne bayan tattaunawar sirrin da suka yi da wasu jigajigan Majalisar Dattawa a ranar Talata. Shugaban NARD na Ƙasa, Emeka Orji, shi ne ya bayyana haka a zantawar da aka yi da shi ta tarho da safiyar wannan Larabar. Sai dai, Orji ya ce za a yi zaman waiwaiye nan da sa'o'i 72 masu zuwa. "Mun gana da Shugaban Majalisar Dattawa da Shugaban Masu Rinjaye da…
Read More
Ƙaƙaba wa Nijar takunkumai ra’ayin ECOWAS ne ba nawa ba – Tinubu

Ƙaƙaba wa Nijar takunkumai ra’ayin ECOWAS ne ba nawa ba – Tinubu

Daga BASHIR ISAH Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa wa'adi da kuma takunkuman da aka ƙaƙaba wa Jamhuriyar Nijar sakamakon juyin mulkin da ya auku a ƙasar, matakai ne da Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS) ta cim ma amma ba ra'ayin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ko Nijeriya ba. Mai magana da yawun Shugaban Ƙasa kan sha'anin yaɗa labarai da hulɗa da jama'a, Mr Ajuri Ngelale shi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa ranar Talata. Ngelale ya ce kuskure ne danganta matakan na ECOWAS da Shugaba Tinubu a matsayin shi kaɗai…
Read More
Yajin Aiki: Gwamnati ta roƙi likitoci da su koma bakin aiki don ceton rayuka

Yajin Aiki: Gwamnati ta roƙi likitoci da su koma bakin aiki don ceton rayuka

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta roƙi Ƙungiyar Likitoci ta Ƙasa (NARD) a kan ta dakatar da yajin aikin da mambobinta ke yi don ceto rayukan marasa lafiya da ke kwance a asibitocin faɗin ƙasar. Babbar Sakatatiyar Ma'aikatar Ƙwadago da Bada Aiki, Mrs Daju Kachallom ce ta yi wannan roƙo sa'ilin da take zantawa da manema labarai ranar Talata a Abuja. Ta ce likitocin su dubi Allah su dubi Annabi, ka da su bari a ci gaba da samun asarar rayukan 'yan Nijeriya a asibitoci saboda rashin samun kulawa. Kachallom ta bai wa likitocin tabbatacin Gwamnatin Tarayya na yin dukkan…
Read More
Alhasan Ɗantata: Mutum mafi arziki a Afirika ta Yamma a shekarar 1950

Alhasan Ɗantata: Mutum mafi arziki a Afirika ta Yamma a shekarar 1950

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Alhassan Ɗantata, fitaccen attajiri a faɗin nahiyar Afirika ta yamma, wanda tushen arzikinsa ya samo asali daga sayar da Goro da Gyaɗa. Haihuwa da nasaba; Alhassan Ɗantata ya fito ne daga cikin zuri’ar Agalawa, iyayensa fatake ne masu yawon kasuwanci daga wannan gari zuwa wancan. An haife shi a shekarar 1877, a wani ƙaramin ƙauye da ake kira Ɗanshayi a garin Bebeji, wanda ke da tazarar aƙalla kilomita goma sha-biyar daga garin Kano. Alhasan ɗaya ne daga cikin ’ya’yan Abdullahi wanda matarsa Fatima da ake kira Amarya ta haifa. Shi Abdullahi ɗa ne ga wani mutum…
Read More
Soke lasisin ‘yan Kannywood: MOPPAN da KSCB sun cimma matsaya

Soke lasisin ‘yan Kannywood: MOPPAN da KSCB sun cimma matsaya

Daga AISHA ASAS Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Malam Abba El-Mustapha ta janye yunƙurinta na ƙaƙaba wa 'yan fim dokar soke lasisinsu da ta shelanta yi a kwanakin baya. Hukumar ta ce, a yanzu za a sabunta wa masu harkar fim rijistansu ne a ƙarƙashin ƙungiyoyin masu shirya finafinai, waɗanda ke ƙarƙashin Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya, wato MOPPAN. Wannan sauyin ya biyo bayan ziyarar da ƙungiyar MOPPAN ƙarƙashin jagorancin shugabanta na ƙasa, Dakta Ahmed Sarari ta kai wa shugaban hukumar ta tace finafinai. Bayanin wanda yake ƙunshe a wata takardar sanarwa ga manema labarai…
Read More
Mutane 1,040 ne suka amfana da tallafin kayan abinci da mawaƙi Rarara ya yi a Katsina

Mutane 1,040 ne suka amfana da tallafin kayan abinci da mawaƙi Rarara ya yi a Katsina

Daga AISHA ASAS Shahararren mawaƙin siyasa, kuma babban mawaƙin Jam'iyyar APC, Dauda Kahutu Rarara, ya bayar da tallafin kayan abinci ga mabuƙata, a ƙoƙarin ganin ya bayar da tasa gudunmawa a samun sasaucin matsin rayuwa da ake ciki. Mawaqin ya bayar da wannan tallafi ne a mahaifarsa, Kahutu da ke Ƙaramar Hukumar Danja, ta Jihar Katsina, kamar yadda babban mai taimaka wa mawaqin a kafafen sada zumunta Rabi'u Garba Gaya ya bayyana. Rabi'u ya ce, Rarara ya gudanar da rabon kayan ne a mahaifarsa da ke Kahutu, sannan an bai wa kowanne mutum ɗaya daga cikin mutanen 1,040 ƙaramin buhun…
Read More
Ƙungiyar Mawaƙan Sabon Rai ta Cocin Ikilisiya sun karrama tsofaffin shugabanin ta

Ƙungiyar Mawaƙan Sabon Rai ta Cocin Ikilisiya sun karrama tsofaffin shugabanin ta

Daga RABI'U SANUSI A ranar Lahadi ne ƙungiyar kai bushara ta mawaƙan sabon rai da ke cocin Ikilisiyar Angilican ta Ƙaramar Hukumar Fagge cikin Jihar Kano ta karrama tsofaffin shugabanin ta da sukai aiki tuƙuru da cigaban yaɗa addini Kiristanci. Kamar yadda tsohon ɗan takarar majalisar jiha na Ƙaramar Hukumar Rogo, kuma mai tsawatarwa a wannan ƙungiya, Hon Haruna Yahaya Kadana ya yi ma manema labarai ƙarin haske jim kaɗan bayan kammala taron karramawar bayan gudanar da addu'o'i kamar yadda aka saba a duk ranakun Lahadin mako. Haruna Kadana ya ce, bai taɓa tunanin zai zama ɗaya daga cikin waɗanda…
Read More
Mutum 45 da Majalisar Dattawa ta tabbatar da su ministoci

Mutum 45 da Majalisar Dattawa ta tabbatar da su ministoci

Daga BASHIR ISAH Biyo bayan tantance su da ta yi, a ƙarshe Majalisar dattawa ta tabbatar da mutum 44 a matsayin ministoci. Waɗanda lamarin ya shafa su ne: -Mohammed Idris Malagi, Neja-Sanata Aliyu Sabi Abdullah, Neja-Nyesom Wike, Ribas-Ekperikpe Ekpo, Akwa Ibom-Sanata Heineken Lolokpobri, Bayelsa-Betta Edu, Cross River-John Enoh, Cross River-Abubakar Momoh, Edo.-Tahir Mamman, Adamawa-Yusuf M Tuggar, Bauchi-Mohammed Ali-Pate, Bauchi-Abubakar Kyari, Borno-Alkali Ahmed Saidu, Gombe-Uba Maigari Ahmadu, Taraba-Sanata Ibrahim Geidam, Yobe-Mohamed Badaru, Jigawa-Mariya Bunkur, Kano-Abdullahi T Gwarzo, Kano-Ahmad Dangiwa, Katsina-Hanatu Musawa, Katsina-Yusuf Tanko Sununu, Kebbi-Atiku Bagudu, Kebbi-Bello M. Goronyo, Sokoto-Mohammed Bello Matawwalle, Zamfara-Hon Nkiru Onyejiocha, Abia-Uju Ohaneye, Anambra-Sanata David Umahi, Ebonyi-Uche…
Read More
Majalisa ta tabbatar da Malagi a matsayin Minista

Majalisa ta tabbatar da Malagi a matsayin Minista

Daga BASHIR ISAH Majalisar Dattawa ta tabbatar da mawallafin Jaridun Blueprint da Manhaja, Mohammed Idris Malagi daga Jihar Neja a matsayin Minista a Gwamnatin Bola Tinubu. Wannan na zuwa ne bayan shafi kimanin mako guda da Majalisar Dattawa ta yi tana tantance sunayen da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya aike mata don naɗa su muƙaman ministoci. Daga cikin waɗanda suka bi sawun Malagi wajen tabbatar da su a matsayin minista har da Dele Alake (Ekiti), tsohon Gwamnan Jihar Ribas Governor Nyesom Wike da tsohon minista a gwamnatin Muhammadu Buhari, Festus Keyamo, SAN, da sauransu. Malagi, Alake da Wike na daga…
Read More