Editor

9216 Posts
INEC tana neman jami’in tattara sakamakon zaɓe a Mafara ruwa a jallo

INEC tana neman jami’in tattara sakamakon zaɓe a Mafara ruwa a jallo

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Hukuma INEC ta jihar Kebbi tana neman jami'in tattara sakamakon zaɓen mazaɓar Marafa bisa ga batan dabo da ya yi ba tare da ya zo yi sanarwar sakamakon ba. Tuni hukumar ta saka wani jami'i a wannan mazaɓar ta Marafa da ke Birnin Kebbi a gundumar Kebbi ta tsakiya da ya ke akwai sakamakon hannun wakilan kowace jam'iyya da kuma ita Kanta hukumar zaɓen.
Read More
Babu inda muka umarci a zaɓi PDP a kujerar Shugaban Ƙasa a Katsina – Lawal Boye

Babu inda muka umarci a zaɓi PDP a kujerar Shugaban Ƙasa a Katsina – Lawal Boye

Daga RABIU SANUSI Rahotanni daga jihar Katsina na bayyana cewa Shugaban Jamiyyar Accord a Jihar Katsina, Salihu Lawal Boye, ya musanta rahotonnin dake cewa Jamiyyar ta goyi bayan ɗan takarar Shugaban Ƙasa na Jamiyyar PDP, Atiku Abubakar, a zaɓen da ya gudana Asabar. Salihu Lawal Boye ya bayyana haka ne alokacin zantawa da manema labarai a Katsina. Ya ce ɗan takarar Gwamnan Jihar Katsina a Jamiyyar Accord wanda ya goyi bayan Alhaji Atiku Abubakar yayi haka ne bada yawun uwar Jamiyyar ba. Yayi kira ga ɗimbin magoya bayan Jamiyyar da su yi watsi da maganganun ɗan takarar Gwamnan Jamiyyar ta…
Read More
Kawu Sumaila ya lashe zaɓen Sanatan Kano ta Kudu

Kawu Sumaila ya lashe zaɓen Sanatan Kano ta Kudu

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Ɗan takarar Sanatan Kano ta Kudu a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar NNPP, Suleiman Abdurrahaman Kawu Sumaila OFR, ya sami nasarar lashe zaɓen sa na zama Sanatan Kano ta Kudu a Majalisar Dattijai ta Tarayya, Farfesa Ibrahim Barde, wanda shi ne babban baturen zaɓe na shekarar 2023 a yankin, shi ne ya bayyana samakon zaɓen a cibiyar tattara sakamakon da ke ƙaramar hukumar Rano. “Kawu Sumaila na jam’iyyar NNPP ya samu ƙuri’u 319,857 inda abokin hamayyarsa Kuma sanata Mai barin gado Kabiru Gaya ya Sami luri'u 192,518. “Saboda haka bayan cika dukkan ƙa'idojin zaɓe, Abdurrahaman Kawu Sumaila…
Read More
Atiku ya lashe Gombe a dukkan ƙananan hukumomi 11

Atiku ya lashe Gombe a dukkan ƙananan hukumomi 11

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya lashe dukkan ƙananan hukumomi 11 na jihar Gombe. A sakamakon zaɓen da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana a safiyar ranar Litinin, jami’ar da ke kula da zaɓen, Farfesa Maimuna Waziri, mataimakiyar shugabar jami’ar tarayya ta Gashua, ta ce Atiku ya samu ƙuri’u 319,123 kan ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, wanda ya samu ƙuri’u 146,977. A sakamakon da aka bayyana daga ƙaramar hukumar Shongom, Atiku Abubakar ya samu ƙuri'u 13,520 yayin da APC ta samu 7,525; Peter…
Read More
Ɗan acaɓa ya lashe zaɓen majalisar wakilai a Kudancin Kaduna

Ɗan acaɓa ya lashe zaɓen majalisar wakilai a Kudancin Kaduna

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An bayyana wani ɗan acaɓa, Donatus Mathew a ƙarƙashin jam'iyyar LP a matsayin wanda ya lashe zaɓen ɗan takarar majalisar wakilai ta Kaura da ke Jihar Kaduna. Da yake bayyana sakamakon zaɓen a jiya, jami’in zaɓen, Farfesa Elijah Ella, ya ce Mathew ya samu ƙuri’u 10,508 inda ya doke ɗan takarar jam’iyyar PDP, Gideon Lucas Gwani wanda ya zo na biyu da ƙuri’u 10,297. A cewar rahotanni, Mathew ya taɓa zama Kansila amma wahala ta tilasta masa zama ɗan acaɓa. An kuma ce shi ɗan Nijeriya ne mai gaskiya kuma mai riƙon amana. Ya ce, ɗan…
Read More
APC ta yi wa PDP ba-zata a Jigawa ta Gabas

APC ta yi wa PDP ba-zata a Jigawa ta Gabas

Daga ABUBAKAR M. TAHEER Jam'iyyar APC mai mulki ta yi nasarar lashe kujerar sanata da ta majalisar wakilai a yankin Jigawa ta Gabas. Yauin zaɓen da ya gudana ranar Asabar, ɗan takarar APC, Ahmed Abdul Hamid Malam Madori, ya samu nasara da ƙuri'u 136,977. Inda ɗan takarar jam'iyyar NNPP, Muhd Garba ya zamo na biyu da ƙuri'a 29,485, sannan Dr. Nuruddeen Muhammad na PDP ya sami ƙuri'a 107,457. Baturen zaɓen, Farfesa Adamu Usman Isge, shi ne ya sanar da hakan inda ya bayyana Ahmed Abdul Hamid a matsayin wanda ya yi nasara. A ɓangaren majalissar wakilan Hadejia, Auyo da Kafin…
Read More
NNPP ta buga ɗan gidan Ganduje da ƙasa, ta lashe zaɓen ɗan majalisa a Kano

NNPP ta buga ɗan gidan Ganduje da ƙasa, ta lashe zaɓen ɗan majalisa a Kano

Daga AMINA YUSUF ALI Abba Abdullahi Umar Ganduje, ɗa a gurin Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya faɗi zaɓen ɗan majalisar wakilai a Kano. Ɗan gidan gwamnan wanda ya fito takarar ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazaɓun Tofa da Rimingado, ya sha ƙasa bayan da abokin karawarsa Tijjani Abudlkadir Jove, ɗan takarar jam'iyyar NNPP ya buga ahi da ƙasa. Jove wanda shi ne wakilin riƙon ƙwarya na wakilcin majalisar, zai maimaita kujerar tasa ne a karo na biyar. An kaɗa wa Jove ƙuri'u 52, 456 yayin da Abba Ganduje shi kuma ya samu ƙuri'u 44,809.
Read More
Ƙanen tshohon Shugaban Ƙasa ‘Yar’adua ya lashe zaɓen sanatan Katsina ta Tsakiya

Ƙanen tshohon Shugaban Ƙasa ‘Yar’adua ya lashe zaɓen sanatan Katsina ta Tsakiya

Daga UMAR GARBA a Katsina Abdul'azizi Musa Yar'adua, ƙane ga tsohon Shugaban Ƙasa marigayi Malam Umaru Musa Yar'adua, ya samu nasarar lashe zaɓen ɗan majalisar dattawa mai wakiltar Katsina ta tsakiya Babban jami'in dake bayyana sakamako farfesa Aminu Ɗalhatu Kankia ne ya sanar da hakan inda ya bayyana cewar 'Yar'adua ya samu ƙuri'a 153,512. Inda ya doke babban abokin hamayyarsa na jam'iyyar PDP, Aminu Surajo Makera wanda ya samu ƙuri'a 152,140. Sai kuma ɗan takarar jam'iyyar NNPP Gambo Abubakar Jally ke mara masu baya da ƙuri'a 1,605 sai kuma Muhammad Mustapha Kurfi na jam'iyyar SDP ya samu ƙuri'a 807 a…
Read More
Mutum 3 sun mutu a harin da aka kai ofishin NNPP a Kano

Mutum 3 sun mutu a harin da aka kai ofishin NNPP a Kano

Daga RABIU SANUSI a Kano Rundunar 'Yan Sandan jihar Kano ta tabbatar da rasuwar mutum biyu yayin da ake tsaka da tattara sakamakon zaɓe a ƙaramar hukumar Tudun Wada dake jihar kano. Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwa da kakakin rundunar 'yan sandan Kano, CP Haruna Abdullahi Kiyawa, ya fitar a ranar Lahadi zuwa safiyar Litinin. Sanarwar ta ce an sami bayanai cewa ana cikin tattara sakamakon zaɓen a Tudun Wada ne cikin ofishin hukumar zaɓe na ƙaramar hukumar wasu gungun 'yan dabar siyasa suka kai hari a ofishin kamfen na ɗan takarar majalisar tarayya tare da cinna masa…
Read More
Al-Makura ya sha kaye a zaɓen Sanatan Nasarawa ta Kudu

Al-Makura ya sha kaye a zaɓen Sanatan Nasarawa ta Kudu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon gwamnan jihar Nasarawa kuma Sanata Umaru Tanko Al-Makura, mai wakiltan Nasarawa ta Kudu a Majalisar Dattawa ƙarƙashin Jam'iyyar APC, ya sha kaye a zaɓensa na sake tsayawa takara a hannun Mohammed Ogishi-Onawo na Jam’iyyar PDP. Da yake bayyana sakamakon zaɓen a ranar Litinin a Lafiya, babban birnin jihar, Farfesa Ahmed Ashiku, jami’in zaɓen, ya bayyana cewa Ogoshi Onawo ya samu ƙuri’u 93,064 inda ya doke Sanata mai ci Al-Makura wanda ya samu ƙuri’u 76,813. Ashiku, yayin da yake bayyana cewa Onawo, bayan ya cika sharuɗɗan doka kuma ya samu mafi yawan ƙuri'u, an…
Read More