Editor

9310 Posts
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta bai wa Tinubu damar bincikar kayayyakin zaɓe

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta bai wa Tinubu damar bincikar kayayyakin zaɓe

Daga BASHIR ISAH Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa (PEPC) mai zamanta a Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja, ta bai wa Hukumar Zaɓe (INEC), umarnin ta bai wa zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa mai jiran gado Bola Tinubu, damar bincikar muhimman kayayyakin da aka yi amfani da su wajen gudanarda zaɓen Shugaban Ƙasa. Tinubu da Jam'iyyar APC sun buƙaci kotu ta ba su damar duba kayayyakin zaɓen ne domin tattara bayanan da za su yi amfani da su wajen kare kansu a kotu daga ƙara da aka shigar a kansu. 'Yan takarar Shugaban Ƙasa na jam'iyyun PDP da Labour, Atiku Abubakar…
Read More
Sanatoci sun karɓi shaidar lashe zaɓensu

Sanatoci sun karɓi shaidar lashe zaɓensu

Daga BASHIR ISAH A ranar Talata Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta miƙa shaidar lashe zaɓe ga sanatocin da suka yi nasara a zaɓen da ya gabta. Shugaban INEC na ƙasa, Mahmood Yakubu, shi ne ya jagoranci miƙa shaidar ga sanatocin wanda ya gudana a Babban Zauren Taro na Ƙasa da Ƙasa da ke Abuja. A jawabin da ya yi ran Asabar da ta gabata, Yakubu ya ce 423 ne suka lashe kujerun majalisun tarayya, yayin da za a sake zaɓe a wasu mazaɓu 46. Waɗanda suka yi nasarar sun haɗa da sanatoci 98 daga cikin 109 da ake da…
Read More
INEC ta miƙa wa zaɓaɓɓun ‘yan Majalisar Wakilai shaidar lashe zaɓe

INEC ta miƙa wa zaɓaɓɓun ‘yan Majalisar Wakilai shaidar lashe zaɓe

Daga BASHIR ISAH Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta miƙa shaidar lashe zaɓe ga 'yan Majalisar Wakilai da suka lashe zaɓe a zaɓen da ya gudana ran 25 ga Fabrairu. A ranar Laraba INEC ta miƙa wa 'yan majalisar shaidarsu a Babban Zauren Taro na Ƙasa da Ƙasa da ke Abuja. Waɗanda suka yi nasarar sun haɗa da sanatoci 98 daga cikin 109 da ake da su, sai kuma 'yan Majalisar Wakilai 325 daha cikin 360 da ake da su.
Read More
Ba mu umarci bankuna su bada tsofaffin takardun kuɗi ba – CBN

Ba mu umarci bankuna su bada tsofaffin takardun kuɗi ba – CBN

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babban Bankin Nijeriya (CBN) a ranar Talata ya ce bai bayar da wani sabon umarni ga bankunan kasuwanci ba kan hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke a ranar Juma’ar da ta gabata na bayar da umarnin a riqa rarraba tsofaffin takardun Naira tare da sabbi har zuwa ranar 31 ga watan Disamba. Kwamitin alqalai na mutane bakwai ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Inyang Okoro, ya bayyana a matsayin wanda ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙasa, akan umarnin da Shugaban Ƙasa ya bada. Muhammadu Buhari ya bai wa Babban Bankin Ƙasar CBN na sake gyarawa…
Read More
Masari ya karɓi jiga-jigan PDP da suka sauya sheƙa zuwa APC

Masari ya karɓi jiga-jigan PDP da suka sauya sheƙa zuwa APC

Daga UMAR GARBA a Katsina Wasu jiga-jigan jam'iyyar PDP tare da magoya bayansu 10,000 sun sauya sheƙa zuwa APC a Jihar Katsina. Akasarin waɗanda suka kwashe kayansu daga jam'iyyar ta PDP zuwa APC na hannun daman tsohon gwamnan jihar ne, wato Ibrahim Shehu Shema. Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari ne ya karɓe su a gidan gwamnatin jihar. Sauya sheƙar na zuwa ne 'yan kwanaki kaɗan kafin gudanar da zaɓen gwamnoni da na 'yan majalisun jihohi a ranar Asabar, 11 ga watan Maris. Daraktan yaƙin neman zaɓen ɗan takarar gwamnan Jihar Katsina Ahmed Musa Ɗangiwa ne ya bayyana wa manema…
Read More
Zaɓen 2023: Ƙalubalen da ke gaban Tinubu

Zaɓen 2023: Ƙalubalen da ke gaban Tinubu

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Yanzu dai ta tabbata, Sanata Bola Ahmed Tinubu, na Jam'iyyar APC shi ne ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2023 da aka gudanar ranar Asabar da ta gabata, da ƙuri'u Miliyan 8 da dubu 794 da 726. Bayan ya samu kashi 25 a cikin ɗari na yawan ƙuri'un da aka kaɗa daga jihohi 30, tare da da samun mafi rinjaye ƙuri'u a jihohi 12 na tarayyar Nijeriya. Shi kuma wanda ya zo na biyu shi ne ɗan takarar shugaban qasa a jam'iyyar adawa ta PDP, Alhaji Atiku Abubakar Wazirin Adamawa, da ya samu ƙuri'u Miliyan 6…
Read More
DSS ta samar da kafafenta a soshiyal midiya

DSS ta samar da kafafenta a soshiyal midiya

Daga BASHIR ISAH Hukumar tsaro ta DSS, ta ce ta ƙirƙiro da shafukan sohiyal domin bunƙasa hanyoyinta na hulɗa da jama'a da masu ruwa da tsaki. Jami'in Hulɗa da Jama'a na hukunar, Dr Peter Afunanya, ne ya bayyana hakan ranar Litinin a Abuja. Ya ce shafukan da suka ƙirƙiro sun haɗa da:Twitter: @OfficialDSSNG Facebook: OfficialDSSNG Instagram: @OfficialDSSNG A cewarsa, shafin Tiwita na PRO na hukumar shi ne: @DrAfunanya_PNA. Ya ce kafin wannan lokaci hukumar ba ta da waɗanan kafafe, kuma tana sa ran soma amfani da su ne daga ranar 6 ga Maris. Jami'in ya ce al'umma su sani cewar,…
Read More
ECOWAS za ta karrama Buhari kan bunƙasa dimokuraɗiyya

ECOWAS za ta karrama Buhari kan bunƙasa dimokuraɗiyya

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Bunƙasa Tattalin Arzikin Ƙasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS), ta ce ta kammala shirinta don karrama Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da lambar yabo saboda nasarorin da ya samu a fannin tsaro da dimokuraɗiyya. Wannan na zuwa ne yayin da Buhari yake shirin kammala wa'adin mulkinsa na biyu. Shugaban ECOWAS kuma Shugaban Ƙasar Guinea Bissau, Umaro Sissoco Embalo, shi ne ya bayyana haka a wajen taron ƙawancen da suka yi yayin da suka haɗu a wajen Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya da aka gudanar a Doha, babban birnin Qatar. Shugaba Embalo ya ce Buhari ya taka rawar gani…
Read More
Mazauna Abuja na fuskantar matsanancin matsalar fetur

Mazauna Abuja na fuskantar matsanancin matsalar fetur

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Yawancin masu ababen hawa a Babban Birnin Tarayya Abuja, na fuskantar matsalar man fetur da dogayen layuka ake cigaba da yi a gidajen man. Wakilin Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya da ya sa ido a gidajen mai a Abuja a ranar Talata, ya ba da rahoton cewa, yawancin gidajen fetur ɗin a rufe suke, yayin da kaɗan ne kawai ke badawa, wanda ya haifar da mummunar cunkoson ababen hawa saboda dogayen layukan da ake yi. Masu motocin sun kuma nuna rashin jin daɗinsu kan ƙarancin tsabar kuɗaɗen da ake samu a ƙasar nan, wanda suka ce…
Read More
Dillalan hatsi sun ƙi amincewa da tiransfa a Abuja

Dillalan hatsi sun ƙi amincewa da tiransfa a Abuja

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Dillalan hatsi a kasuwannin bayan gari a Babban Birnin Tarayya, Abuja, na ƙin amincewa da hada-hadar kuɗi na tiranfa daga kwastomomi, duk da ƙarancin tsabar kuɗi na babban bankin Nijeriya, CBN. Wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya da ya sa ido a kasuwannin Nyanya, Karu, Mararaba da Masaka a ranar Talata a Abuja, ya lura ’yan kasuwar ba sa karɓan tiranfa sai tsabar kuɗi. A cewar ’yan kasuwar, suna sayen kayayyakin ne kai tsaye daga hannun manoman karkara waɗanda ba su yarda da wani nau’i na hada-hadar banki na lantarki ba. Kadijat Ibrahim, ’yar kasuwa a kasuwar…
Read More