Editor

9409 Posts
Da Ɗumi-ɗumu: An kama Manajan Darakta na Kano Line bisa zargin tada rikici a rumfar zaɓe

Da Ɗumi-ɗumu: An kama Manajan Darakta na Kano Line bisa zargin tada rikici a rumfar zaɓe

Daga RABIU SANUSI a Kano Jami’an tsaro a Jihar Kano sun damƙe Manajan Darakta na kamfanin sufuri na jihar, Kano Line, wato Bashir Nasiru Aliko Koki, a mazaɓar Masaƙa dake Ƙofar Mazugal a birnin Kano. Ana zarginsa ne da tayar da tarzoma tare da jagorantar ‘yan daba. Ya zuwa haɗa wannan labarin an miƙa Bashir Nasirshi ga 'yan sanda tare da wasu yaransa uku, sannan mutum sama da 200 sun arce.
Read More
Ni ne zan yi nasara a zaɓen Gwamnan Katsina – Raɗɗa

Ni ne zan yi nasara a zaɓen Gwamnan Katsina – Raɗɗa

Daga UMAR GARBA a Katsina Ɗan takarar Gwamnan Jihar Katsina a ƙarƙashin jam'iyyar APC, Dr. Dikko Umar Raɗɗa, ya ce yana da yaƙinin shi ne zai lashe zaɓen jihar. Raɗɗa ya bayyana haka ne ranar Asabar jim kaɗan bayan da shi da mai ɗakinsa, Hajiya Zulaihat suka kaɗa ƙuri'arsu a mazaɓar Katuka mai lamba 010 da ke mahaifar ɗan takarar dake Ƙaramar Hukumar Charanci ta jihar Katsina. A zantawar da ya yi da manema labarai, Raɗɗa ya ce, "Na zo don kaɗa ƙuri'ata a matsayin haƙƙin ɗan ƙasa. "Ina fata zaɓen zai samar wa al'umar Jihar Katsina shugaba nagari, don…
Read More
Rundunar ‘Yan Sandan Kano ta samu ƙarin kayan aiki

Rundunar ‘Yan Sandan Kano ta samu ƙarin kayan aiki

Daga RABIU SANUSI a Kano Rundundar 'Yan Sandan Jihar Kano ta samu wasu muhimman kayan aiki da za a yi amfani da su wajen Gudanar da zaɓen gwamna a jihar. Daga cikin kayayyakin da Rundundar ta samu sun haɗa jirgin sama mai saukar ungulu wanda zai riƙa shawagi yayin zaɓen. Haka nan, akwai ƙarin jami'an 'yan sanda da kuma motoci da sauransu. Rundundar ta tabbatar wa al'ummar Jihar Kano cewa babu wani mutum da zai samu damar haddasa cikas a yayi zaɓen. Babban Sufeton 'Yan Sanda, Usman Alkali Baba, ya buƙaci rundunar ta yi aiki da kayayyakin yadda ya kamata…
Read More
Ayarin motocin Gwamnan Katsina sun yi hatsari

Ayarin motocin Gwamnan Katsina sun yi hatsari

Daga UMAR GARBA a Katsina Tawagar motocin Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari ta yi hatsari a daren jiya juma'a Hatsarin ya faru ne a kusa da ƙauyen Jiqamshi lokacin da Gwamnan da kuma tawagar motocinsa ke kan hanyar zuwa Ƙaramar Hukumar Ƙafur mahaifar shi inda zai kaɗa ƙuri'arsa a zaɓen gwamna da na 'yan majalisar jiha ranar Asabar. Rahotannin sun ce jami'an tsaro biyu da ke tare da tawagar, Kabir Adamu da Nura Safiyanu, suka rasa rayukansu a yayin da wasu suka jikkata.
Read More
Zaɓen gwamnoni: Sarkin Keffi ya yaba da isowar kayan zaɓe a kan kari

Zaɓen gwamnoni: Sarkin Keffi ya yaba da isowar kayan zaɓe a kan kari

Daga BASHIR ISAH Mai Martaba Sarkin Keffi, Dr Shehu Chindo Yamusa II, ya yaba da yadda tsarin zaɓen wannan karon ya kankama a kan kari. Basaraken ya nuna gamsuwarsa da yadda kayan zaɓen suka iso da wuri aka kuma tantance masu zaɓe a kan kari a zaɓen gwamnoni da majalisun jihohi a ranar Asabar. Sarkin ya bayyana gamsuwarsa ne yayin da yake zantawa da manema labarai a fadarsa jim kaɗan bayna kaɗa ƙuri’arsa a rumfar zaɓe mai lamba 009, Tudun Ƙofa Ward da ke Ƙaramar Hukumar Keffi, Jihar Nasarawa. Ya kaɗa ƙuri’ar tasa ce da misalin ƙarfe 8:42am, tare da…
Read More
Zaɓen gwamnoni: Shugaban Ƙasa mai jiran gado ya kaɗa ƙuri’arsa

Zaɓen gwamnoni: Shugaban Ƙasa mai jiran gado ya kaɗa ƙuri’arsa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa mai jiran gado, Bola Tinubu, ya kaɗa ƙuri'arsa a zaɓen gwamnoni da na majalisun jihohi da ke gudana a wannan Asabar. Kamfanin Dillancin Labarai, NAN, ya rawaito cewar Tinubu ya kaɗa ƙuri'arsa ne da misalin ƙarfe 9:35 na safe a Rumfar Zaɓe 085 a Gunduma 03, da ke Alausa, Ikeja, Jihar Legas. Bayanai sun ce ya yi zaɓen nasa ne cikin yanayi mai tsatssauran tsaro. Matarsa, Oluremi da Sarkin Kasuwa Legas, Cif Folashade Ojo, na daga cikin waɗanda suka take wa Tinubu baya zuwa rumfar zaɓe.
Read More
Rikici ya ɓarke a wurin zaɓe a Bayelsa

Rikici ya ɓarke a wurin zaɓe a Bayelsa

An samu aukuwar rikici a wasu mazaɓu a yankin Ogbia, Jihar Bayelsa a wannan Aasabar da ake gudanar da zaɓen gwamnoni da na'yan majalisun jihohi. Manhaja ta tattaro cewar kayan zaɓen da aka tanada wa gundumar Ogbia ta 2, 3, 4 da ta 5 a Ƙaramar Hukumar Ogbia ta jihar, an lalata su sannan aka yi awon gaba da su. Tuni Gwamnan Jihar, Douye Diri, ya yi tir da wannan ɗanyen aiki. Gwmnan ya yi kira ga Sufeto-Janar na 'Yan Sanda nmda ma Kwamishinan 'Yan Sandan Jihar da su maido da zaman lumana a yankin.
Read More
‘Yan daba sun lalata kayan zaɓe a Taraba

‘Yan daba sun lalata kayan zaɓe a Taraba

Da safiyar Aasabar wasu 'yan daba suka tarwatsa kayan zaɓe a Gundumar Akati cikin Ƙaramar Hukumar Donga, Jihar Taraba. Bayanai daga yankin sun ce lamarin ya faru ne a lokacin da jami'an INEC ke ƙoƙarin raba kayan zaɓe zuwa rumfunan zaɓen yankin. Wakilinmu ya ce tada ƙayar bayan ya yi sanadiyar jama'ar yankin kowa ya tsere don neman mafaka. Wani ganau, Jame Chimi, ya ce zuwan sojoji ne ya taimaka wajen lafar da ƙurar da 'yan dabar suka tayar.
Read More