Editor

9513 Posts
Cutar koron: Zimbabwe ta karɓi tallafin allurar rigakafi daga Chaina

Cutar koron: Zimbabwe ta karɓi tallafin allurar rigakafi daga Chaina

Daga FATUHU MUSTAPHA Rahotanni daga ƙasar Zimbabwe sun nuna jirgin saman da ke ɗauke da allurar rigakafin annobar cutar korona wadda ƙasar Sin ta bayar gudunmawa ga ƙasar ya isa filin jirgin saman ƙasa da ƙasa na Robert Mugabe da ke Harare, babban birnin kasar, da asubahin wannan Litinin. Da yake jawabi a filin jirgin, Mataimakin Shugaban Ƙasar Zimbabwe Constantino Chiwenga, ya ce ƙasar Sin ta jima tana taimaka wa Zimbabwe kan sha'anin yaƙi da annobar korona, kuma gudunmawar rigakafin zai taimaka wa ƙasar a yaƙin da take yi da annobar. Kazalika, Chiwenga ya ce gudunmawar za ta yi tasiri…
Read More
‘Yan fashin daji na shirin mallakar makamai masu linzami, inji Sheikh Gumi

‘Yan fashin daji na shirin mallakar makamai masu linzami, inji Sheikh Gumi

Daga WAKILIN MU An bayyana cewa 'yan fashin daji da ke dazuzzakan jihohin Arewa suna shirin mallakar makaman kakkaɓo jirgin yaƙi domin daƙile hare-haren sojoji. Sheikh Abubakar Gumi ne ya bayyana haka a wata tattaunawa da jaridar PUNCH ta yi da shi. A kwanankin baya ne Gumi ya ziyarci 'yan ta'addar a dajin Zamfara ya gana da su inda suka nuna suna satar mutane suna karɓar fansa ne domin tara kuɗaɗen sayen makamai. Bayan dawowarsa, Gumi ya yi kira ga gwamnati da ta duba ta yi wa ɓarayin afuwa domin ba su damar ajiye makamansu. Yayin ziyarar tasa Gumi ya…
Read More
Kamfanin BUA ya samu ribar bilyan N95 a 2020

Kamfanin BUA ya samu ribar bilyan N95 a 2020

Daga AISHA ASAS Kamfanin sarrafa siminti na BUA, ya bada sanarwar cewa ya tara kuɗaɗen shiga har naira bilyan N209 a 2020 inda ya ce ya samu ƙarin kashi 19 cikin 100 idan aka kwatanta da abin da ya tara 2019. Haka nan, kamfanin ya ce a bara ya samu ribar naira bilyan N95.4 wanda a cewarsa hakan ya ɗara ribar da ya samu a 2019 da kashi 16 cikin 100 inda ya samu naira bilyan N82.4. Duka waɗannan bayanai na ƙunshe ne cikin sanarwar da ta fito ta hannun Shugaban Sashen Sadarwa na Kamfanin, Sunday Ogieva, wadda Manhaja ta…
Read More
Wasan dambe: Usman ya lashe  kambun UFC karo na uku

Wasan dambe: Usman ya lashe kambun UFC karo na uku

Daga WAKILIN MU Dan wasan damben nan Kamaru Usman, wanda ɗan asalin Nijeriya ne, ya sake lashe kambunsa na UFC bayan da ya doke Gilbert Burns daga ƙasar Brazil a karawar da suka yi a Lahadin da ta gabata. Wannan shi ne karo na uku da Usman ke samun nasarar lashe wannan kambu. Ya samu nasarar farko ne a 2019 bayan da ya doke Colby Covington, sai ta biyu da ya samu a 2020 bayan da ya doke Jorge Masvidal. Yayin wasan baya-bayan nan, Usman bai yi wa Burns da wasa ba inda ya bambance masa tsakanin aya da tsakuwa.…
Read More
‘Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji 21 a Neja

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji 21 a Neja

Daga AISHA ASAS Masu satar mutane a jihar Neja sun kama mota (bas) sukutum mallakar gwamnatin Neja (NSTA) ɗauke da fasinjoji 21 a daidai ƙauyen Yakila a cikin ƙaramar hukumar Rafi. Bayanan da Manhaja ta samu, sun nuna motar ta fito ne daga garin Kontagora zuwa Minna, babban birnin jihar, inda ɓarayin suka tare ta a hanya. Sannan fasinjoji 21 da ke cikin motar, ɓarayin sun tasa ƙeyarsu zuwa cikin daji, suna yi suna harbin bindiga a iska, lamarin da ya razana mazauna ƙauyen inda kowa ya yi gudun neman mafaka. Bayanai sun nuna yankin Yakila ya zama tamkar maɓuyar…
Read More
Oyo: Makinde ya rufe kasuwar Shasha saboda ɓarkewar rikici

Oyo: Makinde ya rufe kasuwar Shasha saboda ɓarkewar rikici

Gwamman jihar Oyo, Engr. Seyi Makinde, ya bada umarnin rufe kasuwar Shasha da ke Ibadan har sai abin da Allah Ya yi biyo bayan ɓarkewar rikici a tsakanin 'yan kasuwan kasuwar. Kazalika, gwamnan ya sanya dokar taƙaita zirga-zirga a ciki da kewayen ƙaramar hukumar Akinyele sakamakon zaman ɗar-ɗar da jama'a ke yi a yankin da kasuwar take. Duka wannan ya faru ne a ranar Asabar, 13/02/2021. Sanarwar da ta fito daga ofishin Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnatin Jihar, Mr. Taiwo Adisa, ta nuna Gwamna Makinde ya ɗauki wannan mataki ne domin lafar da ƙurar da hargitsin ya tayar. Sakataren…
Read More
Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint ya sabunta rajistarsa a APC

Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint ya sabunta rajistarsa a APC

Daga FATUHU MUSTAPHA A Juma'ar da ta gabata Shugaban Jaridun Manhaja da Blueprint, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ya sabunta rajistarsa ta zama ɗan jam'iyyar APC a rumfar zaɓensa da ke Malagi, a ƙaramar hukumar Gbako da ke jihar Neja. Bayan kammala rajistarsa, Alhaji Idris ya yaba da yadda aikin yin rajistar ke guna cikin lumana a rumfar zaɓensu, tare da kira ga 'yan jam'iyyarsu ta APC a faɗin jihar kan kowa ya tabbatar da ya yi rajista ko sabunta rajistarsa. Yana mai cewa, "Na yi matuƙar farin ciki da yadda aikin yin rajistar ke gudana. Wannan wata alama ce mai…
Read More
Masarautar Zazzau ta naɗa ɗanjarida a matsayin Ɗan Iiyya

Masarautar Zazzau ta naɗa ɗanjarida a matsayin Ɗan Iiyya

Daga WAKILIN MU Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, ya naɗa Alhaji AbdulRahaman Nuhu Bayero a matsayin sabon Ɗan Iyyan Zazzau. AbdulRahaman Nuhu Bayero ya maye gurbin marigayi Ɗan Iyan ne wanda ya rasu a Nuwamban 2020. Wasiƙar naɗin wadda ta sami sa hannun Sakataren Sarkin Zazzau kuma Sarkin Fulanin Zazzau, Alhaji Barau Musa Aliyu, ta nuna kwamitin naɗi zai sanar da ranar da bikin naɗin zai gudana. Masarautar ta taya AbdulRahaman Nuhu Bayero murnar samun wannan muƙami tare da addu'ar Allah ya taimaka masa. Sabon Ɗan Iyyan, ma'aikaci ne a sashen labaru da al'amuran yau a babban ofishin Radio…
Read More
Ganduje ya rantsar da sabbin ciyamomi a Kano

Ganduje ya rantsar da sabbin ciyamomi a Kano

Daga AISHA ASAS Gwamnatin Jihar Kano ta rantsar da sabbin zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomin jihar su 44 a Juma'ar da ta gabata. Sa'ilin da yake jawabi yayin bikin rantsarwar, Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya ce cika aiki shi ne babban abin da gwamnatinsa ta fi maida hankali a kai. Tare da kira a gare su da su kasance masu ƙwazo da kuma yin aiki da gaskiya. A cewar gwamnan, ƙanan hukumomi a matsayin mataki na uku na tsarin gwamnati na buƙatar jajirtattun shugabanni da za su yi aiki tukuru. Yana mai cewa sadaukarwa da kuma cika aiki su ne…
Read More
Nijeriya za ta ƙirƙro rigakafin korona ba da daɗewa ba, cewar Minista Onu

Nijeriya za ta ƙirƙro rigakafin korona ba da daɗewa ba, cewar Minista Onu

Daga BASHIR ISAH Ministan Kimiyya da Fasaha Ogbonnaya Onu, ya ce nan ba da daɗewa ba Nijeriya za ta ƙirƙiro maganin rigakafin cutar korona don amfanin 'yan ƙasa. Ministan ya ce hakan zai samu ne ta dalilin tawagar ƙwararrun kimiyya da aka kafa ƙarkashin jagorancin Dr Oladipo kolawole na Jami'ar Adeleke, inda tawagar ke kan gudanar da bincikenta kan maganin cutar korona. Onu ya bayyana haka ne a Abuja a lokacin da ya karɓi baƙuncin wani kwamitin masana kimiyya a Abuja. Ministan ya yaba wa tawagar masu binciken daga Jami'ar Adeleke bisa sanya sunan Nijeriya a jerin ƙasashen duniya masu…
Read More