Editor

9513 Posts
Za a ƙaddamar da littafin salatin Annabi a ranar Asabar a Kano

Za a ƙaddamar da littafin salatin Annabi a ranar Asabar a Kano

Daga FATUHU MUSTAPHA A ranar Asabar mai zuwa, 20 ga Fabrairu, 2021, za a ƙaddamar da wani littafi da aka wallafa a kan salatin Annabi Muhammadu (SAW) a Kano. Littafin, mai taken 'Salatin Annabi Muhammadu Sallallahu Alaihi Wa Sallam: Matsayinsa Da Fa'idojinsa Da Sigoginsa', wata marubuciya mai suna Hajiya Hajara Muhammad Kabir ce ta wallafa shi. Ɗan kwamitin yaɗa labarai na shirya taron, Malam Ibrahim Sheme, ya bayyana cewa za a ƙaddamar da shi ne a fadar Mai Martaba Sarkin Kano da ƙarfe 10 na safe. A cikin takardar sanarwa ga manema labarai, Sheme ya ce manyan baƙi daga sassa…
Read More
Neja: Bello ya tabbatar da sace ɗalibai 27 da wasu mutum 15 a yankin Kagara

Neja: Bello ya tabbatar da sace ɗalibai 27 da wasu mutum 15 a yankin Kagara

Daga BASHIR ISAH Gwamnan jihar Neja Abubakar Sani Bello, ya tabbatar da 'yan bindiga sun sace ɗaliban Kwalejin Kimiyya ta Gwamnati da ke Kagara su 27 da ma'aikatar makarantar 3 da kuma wasu mutum 12, a garin Kagara cikin ƙaramar hukumar Rafi, jihar Neja. Bello ya tabbatar da faruwar haka ne ga manema labarai a ranar Laraba jim kaɗan bayan kammala taron gaggawa da shugabannin tsaro a Minna, babban birnin jihar. Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), ya ruwaito cewa 'yan bindigar sun shiga makarantar ne da misalin ƙarfe biyu na daren Laraba, inda suka kashe ɗalibi guda da sace…
Read More
Rikicin Kasuwa: Gwamnonin sun ziyarci Shasha

Rikicin Kasuwa: Gwamnonin sun ziyarci Shasha

Daga WAKILIN MU Gwamnan jihar Kebbi Abubakar Bagudu, ya ce Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) ta yinƙura domin mara wa Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo baya wajen dawo da zaman lafiya a kasuwar Shasha da ke Ibadan, bayan hargitsin da ya auku a kasuwar cikin makon da ya gabata. Bagudu ya faɗi haka ne a Talatar da ta gabata, sa'ilin da yake magana da manema labarai yayin ziyarar gani da ido da shi da wasu takwararorinsa suka kai kasuwar. Tawagar gwamnonin da ta yi wannan ziyara ta ƙunshi Gwamna Bagudu na jihar Kebbi da Abdulahi Ganduje na jihar Kano da…
Read More
Yadda na sayar da kadarorina don bada tallafin karatu ga ɗaliban Kano 370 – Kwankwaso

Yadda na sayar da kadarorina don bada tallafin karatu ga ɗaliban Kano 370 – Kwankwaso

Daga AISHA ASAS Gwamnan Jihar Kano na dauri, Rabiu Kwankwaso, ya bayyana yadda ya sayar da wasu kadarorinsa domin ɗaukar nauyin ɗalibai 'yan asalin Kano su 370 zuwa karatu a ƙasashen ƙetare a ƙarƙarshin Gidauniyar Kwankwasiyya. Kwankwaso ya bayyana haka ne a lokacin da ya je tarbar ɗaliban da suka ci gajiyar shirin da suka dawo daga Indiya da Dubai a babban filin jirgin sama na Malam Aminu Kano, inda ya bayyana gamsuwarsa dangane da ayyukan gidauniyar. Tsohon Ministan Tsaron ya ce a lokacin da ya yanke shawara kan batun ɗaukar nauyin ɗaliban sai ya ji ya gamsu da ya…
Read More
Nijeriya: An samu ƙaruwar matsalolin tsaro a ‘yan makonnin da suka gabata – Abdulsalami

Nijeriya: An samu ƙaruwar matsalolin tsaro a ‘yan makonnin da suka gabata – Abdulsalami

Daga FATUHU MUSTAPHA Tsohon Shugaban Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Zaman Lafiyar Ƙasa (NPC), General Abdulsalami Abubakar, ya ce a tsakanin makonni biyun da suka gabata matsalar rashin tsaro da rashin haɗin kai sun ƙaru a sassan Nijeriya. Don haka ya yi kira ga gwamnoni da su gyara ɗarama sannan su maganace waɗannan matsaloli da ke faruwa a jihohinsu. Abdulsalam ya yi kira ga 'yan ƙasa da a kasance masu haƙuri da juriyar mawuyacin halin da aka shiga, sannan a zamo masu sadaukarwa wajen daidaita lamurran ƙasa. Tsohon Shugaban Ƙasar ya yi wannan gargaɗi ne yayin ganawar da ya yi da…
Read More
Bawa ya kama hanyar kafa tarihi a hukumar EFCC

Bawa ya kama hanyar kafa tarihi a hukumar EFCC

Daga FATUHU MUSTAPHA A halin da ake ciki, Abdulrasheed Bawa, ɗan shekara 40, ya kama hanyar kafa tarihi na zama mai mafi ƙarancin shekaru da zai shugabanci Hukumar Yaƙi da Zambar Kuɗaɗe da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa (EFCC). A ranar Talata Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa sunan matashin don neman amincewarta kan naɗa shi sabon shugaban EFCC. Bayanai sun nuna Bawa ƙwararre ne a fannin bincike dangane da batutuwan da suka shafi maguɗin kuɗi da sauran laifuka da suka danganci tattalin arziki. Tun bayan dakatar da shugaban riƙo na EFCC Ibrahim Magu, a ranar…
Read More
Za mu yi maganin masu haifar da rikice-rikice a ƙasa, inji Buhari

Za mu yi maganin masu haifar da rikice-rikice a ƙasa, inji Buhari

Daga AISHA ASAS Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ɗora alhakin faruwar wasu rikice-rikice a sassan ƙasar nan kan attajirai da masu matsayi, tare da shan alwashin yin maganinsu. Buhari ya yi wannan magana ne a ranar Talata a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar dattawan Barno da Yobe a fadarsa da ke Abuja kamar dai yadda mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Femi Adesina ya bayyana. A sanarwar da Femi ya fitar Buhari ya ce, "Muna da buƙatar wannan ƙasa, za mu ci gaba da aiki domin samun daidaito. "Ina da yaƙinin cewa za mu shawo kan 'yan…
Read More
Kwamiti ya yi zaman farko don magance rashin zuwan yara makaranta

Kwamiti ya yi zaman farko don magance rashin zuwan yara makaranta

Daga FATUHU MUSTAPHA Kwamitin Gudanarwa kan Shirin Sabuwar Hanyar Bada Karatu (National Steering Committee on Alternate School Programme) ya yi taron sa na farko a ranar Litinin a Gidan Ma'aji (Treasury House) da ke Abuja. Taron ya fara aiwatar da tsare-tsare kan hanyoyin da za a bi a magance matsalolin da ke sanya yara su daina zuwa makaranta a Nijeriya tare da gaggauta rage yawan irin waɗannan yaran ta hanyar sama masu ilimin farko mai inganci da ilimin sana'o'in a wasu yanayi na musamman waɗanda ba a magance su a tsarin da ake da shi a yanzu ba. A jawabin…
Read More
Okonjo-Iweala ta zama shugabar WTO

Okonjo-Iweala ta zama shugabar WTO

Daga AISHA ASAS Majalisar Ƙoli ta Ƙungiyar Cinikayya ta Duniya (WTO), ta tabbatar da Dr. Ngozi Okonjo-Iweala daga Nijeriya a matsayin Babbar Daraktar ƙungiyar. Da wannan, Okonjo-Iweala ta zama ta bakwai kenan daga jerin waɗanda suka riƙe wannan muƙami. Ranar 1 ga watan Maris ake sa ran Okonjo-Iweala za ta kama aiki, inda za ta kasance mace ta farko daga Nahiyar Afirka da ta taɓa ɗarewa kan muƙamin. Za ta riƙe wannan muƙami ne na tsawon shekaru huɗu masu zuwa, wato dai wa'adinta zai ƙare ne ya zuwa 31 ga Agustan 2025. A cewar Shugaban Majalisar ƙungiyar, David Walker daga…
Read More
Mutanen Neja sun yi murna da shirin tallafin Gwamnatin Tarayya ga matan karkara

Mutanen Neja sun yi murna da shirin tallafin Gwamnatin Tarayya ga matan karkara

Daga WAKILIN MU Gwamnan Jihar Neja, Alhaji Abubakar Sani Bello, ya bayyana farin cikin sa kan yadda aka raba kuɗi naira miliyan tamanin ga matan jihar su 4,000 a ƙarƙashin shirin tallafa wa matan karkara da jari wanda Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa. Gwamnan ya faɗi haka ne lokacin da Ministar Harkokin Jinƙai Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta kai ziyara a jihar a ranar Asabar. Gwamnan ya ce shirin na 'Cash Grant for Rural Women' zai taimaka wa matan jihar da dama wajen ficewa daga ƙangin fatara da yunwa. Gwamnan, wanda Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Ahmed Ibrahim…
Read More