Babaji

4782 Posts

Peter Obi ya magantu kan hukuncin kotu na soke rajistar NDC

Jam’iyyar NDC ta bayyana cewa za ta ɗaukaka ƙarar hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja ta yanke na soke umarnin da ya tilasta wa INEC yin rajistar jam’iyyar. A cewarta, ba a soke rajistarta ba, kuma dukkan ayyukanta za su ci gaba kamar yadda aka saba. Hukuncin da Mai Shari’a Isah Dashen ya yanke ya soke hukuncin da kotun ta bayar a watan Disambar 2025, bayan wata ƙungiya mai suna Peace Movement Party ta yi iƙirarin cewa tambarin da aka yi amfani da shi wajen rajistar NDC nata ne. Shugaban NDC na ƙasa, Moses Cleopas, ya ce jam’iyyar…
Read More

Rashin tsaro: Rundunar sojoji za ta ɗauki mutum 28,000 aiki

Rundunar Sojojin Nijeriya ta kammala shirye-shiryen ɗauka da horas da ƙarin sojoji 28,000 domin kara karfafa yaki da matsalolin rashin tsaro da ke addabar sassan kasar. Babban Hafsan Sojojin Kasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a, 26 ga Yuni 2026, yayin wani taron manema labarai da aka shirya domin karrama Ranar Sojojin Nijeriya (NADCEL 2026). A cewarsa, rundunar tana fadada tsarinta, tana inganta dabarun tura sojoji zuwa wuraren aiki, tare da amfani da fasahohin zamani domin fuskantar sabbin barazanar tsaro da ke tasowa a Nijeriya. Janar Shaibu, wanda Babban Jami’in Tsare-tsare da Manufofi na Rundunar…
Read More

Kofin Duniya: Ingila, Portugal, Ghana, Misra da Paraguay sun haye zuwa zagayen ‘yan 32

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙasashen Ingila, Portugal, Ghana, Misra da Paraguay sun yi nasarar tsallakewa zuwa zagayen 'yan 32 a gasar Kofin Duniya da ke cigaba da gudana a Nahiyar Amurka. Duk cewa, Ingila, Portugal Ghana da Misra suna da sauran wasa guda-guda a zangon rukunin-rukuni, sakamakon wasannin da aka buga a yanzu sun nuna cewa sun riga sun yi nasarar tsallakewa zuwa zagaye na gaba a gasar, wanda aka faɗaɗa adadin ƙasashensa zuwa 48. Paraguay ce ƙasa ɗaya daga cikin biyar ɗin da ta kammala buga wasanninta uku na rukunin, inda ta samu maki huɗu da suka…
Read More

Kano: Da katin zaɓe ake tabbatar da jagoranci nagari – Maifata

Kwamitin Wayar da Kan Al'umma game da mahimmancin Katin Zaɓe, a ƙananan hukumomi 44 dake faɗin jihar Kano, ya yi gangamin taro na masu ruwa da tsaki kan al'amuran jama'a, tare da haɗakar Ƙungiyoyin Aikin Gayya na ƙananan hukumomi 8 a Sakatariyar Ƙaramar Hukumar Bichi. Ƙananan hukumomin sune Ɓagwai, Bichi, Dawakin Tofa, Ghari, Rimin Gado, Shanono, da kuma Tsanyawa. Shugaban Majalisar ƙaramar hukumar da ya karɓi baƙuncin wannan tawaga, Alhaji Hamza Sule Maifata, ya ja hankalin al'umma da su mayar da hankali wajen fitowa yin rijistar katin zaɓen ga waɗanda ba su samu ikon yi ba, bisa la'akari da wannan…
Read More

Gidauniyar Sidiya Charity ta ƙaddamar da shirin horar da mata sa’o’i don ƙarfafa tattalin arziƙi

A wani muhimmin mataki na inganta rayuwar al’umma, an ƙaddamar da Women Empowerment Training Initiative, wani shiri da Sidiya Charity Foundation ta assasa domin bai wa mata damar koyon sana’o’i da dabarun dogaro da kai, tare da ƙarfafa musu gwiwar zama masu cin gashin kansu a fannin tattalin arziki. An gudanar da bikin ƙaddamarwar ne cikin yanayi na farin ciki da fatan alheri, inda manyan baƙi, masu ruwa da tsaki, shugabannin al’umma da sauran masu goyon bayan ayyukan ci gaba suka halarta domin nuna goyon bayansu ga wannan gagarumin shiri. Da take jawabi a wajen taron, Shugabar Gidauniyar, Hajiya Sadiya…
Read More

Peter Obi ya shiga tsaka-mai-wuya bayan kotu ta soke rajistar NDC

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A wani mataki da ake ganin babban koma-baya ne ga ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, wata Babbar Kotun Tarayya a Lokoja ta soke hukuncinta na baya da ya umarci Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta yi wa NDC rajista a matsayin cikakkiyar jam’iyyar siyasa. Mai shari’a Isah Dashe ne ya yanke hukuncin bayan ya amince da ƙorafin da jam'iyyar Peace Movement Party (PMP) ta shigar, ranar Juma'a. Da wannan hukunci, umarnin da kotun ta bayar a baya na tilasta wa INEC rajistar jam’iyyar NDC ya zama babu tasiri, lamarin da…
Read More

Har yanzu INEC ba ta samu kuɗin zaɓe ba yayin da wa’adin Yuli ya ƙarato, ta ce za ta yi zaɓen shugaban ƙasa na gwaji

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Ƙasa INEC, ta bayyana cewa har yanzu ba ta karɓi kuɗaɗen da aka ware domin gudanar da babban zaɓen shekarar 2027 ba. Kwamishinan INEC mai kula da wayar da kan masu kaɗa ƙuri’a da yaɗa labarai, Mohammed Haruna ne ya bayyana hakan a wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Abuja. Ya ce duk da cewa ba a saki kuɗaɗen ba, hukumar ta fara shirye-shiryen zaɓen 2027, ciki har da sayen sabbin na’urorin tantance masu kaɗa ƙuri’a na BVAS da maye gurbin waɗanda suka lalace ko suka ɓace a zaɓukan baya.…
Read More

Zamfara: Gwamna Lawal ya ci alwashin ƙarin tallafi ga dakarun tsaro don daƙile ayyukan ta’addanci

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake tabbatar da aniyar gwamnatinsa na ci gaba da bai wa jami’an tsaro cikakken goyon baya domin ƙarfafa yaƙi da matsalolin tsaro a faɗin jihar. Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin da ya jagoranci taron mako-mako na Majalisar Tsaro ta Jihar Zamfara da aka gudanar a Fadar Gwamnati da ke Gusau. A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa taron ya haɗa shugabannin dukkannin hukumomin tsaro da ke aiki a jihar. Sanarwar ta ce, mahalarta taron sun tattauna hanyoyin ƙara ƙarfafa ayyukan…
Read More

Kofin Duniya: Moroko ta karya tarihin Super Eagles na ƙasar Afirka mafi yawan ƙwallaye

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙasar Moroko ta kafa sabon tarihi na zama ƙasar Afirka da ta fi yawan ƙwallaye a gasar Kofin Duniya na FIFA, lamarin da ya ba ta damar kere Super Eagles ta Nijeriya. Ƙasar ta samu nasarar haka ne bayan doke Haiti da ci 4 da 2 a gasar, sakamakon da ya ba ta damar zuwa zagayen 'yan 32 a gasar. Waɗannan ƙwallaye da Moroko ta samu sun ba ta damar kere a Nijeriya a matsayin ƙasar da ta fi yawan ƙwallaye a gasar daga ƙasashen Nahiyar Afirka. A yanzu, Atlas Lions tana da ƙwallo…
Read More

Kofin Duniya: Ivory Coast ta haye zuwa rukunin ƙalubale bayan doke Curaçao

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Tsohon ɗan wasan Arsenal, Nicolas Pepe ya zura ƙwallo biyu a raga a wasan da Cote d'Ivoire ta yi da Curaçao a gasar Kofin Duniya na 2026, lamarin da ya ƙasar Afirkan damar hayewa zuwa rukunin ƙalubale. Pepe na ɗaya daga cikin 'yan wasan da aka sauya daga waɗanda suka sha kaye da ci 2 da 1 a hannun Jamus a wasa na biyu na matakin rukunin-rukuni. A yanzu dai, Ivory Coast za ta haɗu da wanda ya ƙare a matsayi na uku daga rukunin I a birnin Dallas a ranar 30 ga Yuni.
Read More