Babaji

4782 Posts

Kofin Duniya: Ecuador ta tsallake zuwa zagayen ‘yan 32 bayan doke Jamus

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A cigaba da fafatawa a gasar Kofin Duniya na 2026, ƙasar Ecuador ta yi nasarar hayewa zuwa zagayen 'yan 32 bayan doke Jamus da ci 2 da 1 a wasan ƙarshe na rukunin E a ranar Alhamis. Ita ma Jamus, wadda ta lashe kofin har sau huɗu a tarihinta, ta tsallake zuwa zagayen bayan samun nasara a wasa biyun farko. Lorey Sane na Jamus ne ya fara zura ƙwallo a ragar Ecuador a zangon farko na wasan, inda daga bisani ƙasar Nahiyar Amurkan ta farke da kuma ƙara ƙwallo ta biyu a raga. Wannan…
Read More

Abin da ya sa nake son a koro ‘yan wasan Real Madrid daga gasar Kofin Duniya – Mourinho

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Sabon kocin ƙungiyar Real Madrid, Jose Mourinho ya yi fatan a koro 'yan wasan ƙungiyar daga gasar Kofin Duniya na 2026 da wuri saboda su mayar da hankali akan wasannin gabanin sabuwar kaka cikin tsanake. Mourinho ya bayyana haka ne a wata hira ta wani shiri da aka gudanar ta BeastModeOn inda ya tattauna akan muhimman ƙalubalen da manyan ƙungiyoyi suke fuskanta yayin da ake buga manyan gasa na ƙasa da ƙasa. Daga cikin 'yan wasan ƙungiyar da ke buga gasar Kofin Duniya na 2026 akwai Kylian Mbappe, Vinicius Junior, Aurelien Tchouameni, Antonio Rudiger…
Read More

Gwamnatin Kano da ‘yan sanda sun ƙaddamar da binciken mutuwar ɗalibar St. Louis, Nihal

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya amince da kafa kwamiti na musamman domin gudanar da bincike akan ababen da suka yi sanadiyyar mutuwar wata ɗaliba ta makarantar St. Louis College da ke Kano. Kakakin gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ne ya sanar da haka a ranar Alhamis a Kano, cikin wata takarda. Ya ce, Alhaji Ali Makoɗa, Kwamishinan Ilimin jihar ne zai jagoranci kwamitin, wanda ya ƙunshi masu ruwa da tsaki a fanin ilimi, shari'a, makarantun kuɗi da kuma wakilan makarantar da abin ya shafa. Sauran mambobin kwamitin sun haɗa da Aminu…
Read More

CBN ya umarci a riƙe asusun da aka alaƙanta da ayyukan ta’addanci a Nijeriya

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Babban Bankin Nijeriya CBN, ya umarci dukkan bankuna da cibiyoyin kuɗi a Nijeriya da su gaggauta riƙe asusu da kadarorin da aka danganta su da mutane shida da wasu ma'aikatan kasuwar canji (BDC) su huɗu bisa zargin su da ɗaukar nauyin ta’addanci. A ranar 24 ga Yuni, 2026 ne bankin ya fitar da umarnin a takarda mai ɗauke da lamba kamar haka: Ref: CMD/FCS/PUB/CIR/002/011, inda ya ce za a fara aiwatar umarnin ne akan jaddawalin waɗanda gwamnatin Nijeriya ta fitar da sunayensu akan batun hannu a ta'addanci. CBN ya ce, yana sanar da cibiyoyin…
Read More

An ceto mutum 10 bayan ruftawar gini a Legas

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kimanin mutane 10 ne aka ceto bayan samun raunuka a sanadiyyar ruftawar wani gini a yankin Alakija da ke Jihar Legas a safiyar ranar Alhamis. Rahotanni sun bayyana cewa, hukumar kashe gobara da bayar da agajin gaggawa ta jihar ta ce al'amarin ya faru ne a ranar Alhamis, a yankin hanyar Old Ojo ta madakatar ababen hawa daura da babban titin Legas zuwa Badagry. Kwantirola Janar ta hukumar, Margaret Adeseye ta ce iftila'in ya rutsa ne da wani gida da ke da mutane da dama suke zama acikinsa, kamar yadda ta shaida a wata…
Read More

Adadin mamatan girgizar ƙasar Venezuela ya kai 164 yayin da ake ci gaba da ceto waɗanda suka tsira

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Aƙalla mutane 164 ne suka rasa rayukansu yayin da 971 suka jikkata a sakamakon iftila'in girgizar ƙasa guda biyu da ya auku a ƙasar Venezuela, lamarin da ya haifar da rushewar gine-gine da tilasta wa hukumomin tsaro ayyana dokar ta-ɓaci. Shugabar riƙo ta ƙasar, Delcy Rodriguez ta ce al'amarin ya auku ne a cikin daƙiƙa 40 a ranar Laraba da dare. Wannan girgizar ƙasa ita ce mafi muni a tsawon sama da shekara 100 da ta samu ƙasar kudancin Amurkan, kamar yadda rahotanni suka bayyana. Yankin La Guaira, wato arewacin babban birnin ƙasar Caracas…
Read More

ICPC ta gurfanar da El-Rufa’i da wasu shida kan badaƙalar kwangilar N8.68bn na kyamarorin tsaro

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ICPC, ta gurfanar da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, tare da wasu shida bisa tuhume-tuhume guda 11 masu alaƙa da zargin rashawa, halasta kuɗaɗen haram da sauran laifuffuka masu alaƙa da badaƙalar kwangilar kyamarorin tsaro. Sauran waɗanda ake tuhuma tare da El-Rufai sun haɗa da Jimi Lawal, da kuma kamfanonin singularitynetworksecurity.com, Solar Life Nigeria Limited, Knowledge Investment Nigeria Limited, Intercellular Nigeria Limited da Noble Coast Resources Limited. Haka kuma, ICPC ta wallafa a shafinta na yanar gizo cewa Bashir El-Rufai, wanda wa ne ga El-Rufa'i ana…
Read More

Kofin Duniya: Brazil, Moroko da Afirka ta Kudu sun haye zuwa zagayen ‘yan 32

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙasar Afirka ta Kudu ta yi nasarar hayewa zuwa rukunin 'yan 32 a gasar Kofin Duniya na 2026, a karo na farko a tarihinta bayan doke Koriya ta Kudu da ci 1 da 0 a wasansu na ranar Laraba. Ƙasar Afirkan ta yi nasarar samun zuwa zagayen ne bayan kammala wasannin rukunin-rukuni na rukuninsu da ke gudana a gasar, inda suka ƙare a matsayi na biyu. A wani ɓangare kuwa, Brazil ta Nahiyar Amurka ta Kudu ta tsallake zuwa zagayen ne bayan da ta lallasa Scotland da ci 3 da 0, lamarin da ya…
Read More

Girgizar ƙasa ta yi ajalin mutane da dama da jikkata ɗaruruwa a Venezuela

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wasu tagwayen girgizar ƙasa sun yi sanadiyyar mutuwar sama da mutum 80 da jikkata 700 da ɗoriya a Venezuela, kamar yadda shugabar riƙo ta ƙasar ta bayyana a ranar Alhamis, lamarin da ya jefa jama’ar yankin cikin firgici. Akan haka ne jami'an hukumomi da sauran al'ummar ƙasar suka riƙa hawa abubuwa masu tsawo da nufin neman tsira daga iftila'in, lamarin da ya sa jagoran, Delcy Rodriguez ta ayyana dokar ta-ɓaci. Girgizar ƙasar masu faɗin murabba'i 7.2 da 7.5 sun auku ne a waje guda na Venezuela a ranar Laraba, kamar ya yadda hukumomi suka…
Read More

Ina son barin Atletico Madrid, inji Alvarez

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ɗan wasan gaba na ƙasar Argentina, Julian Alvarez ya tabbatar da aniyarsa ta ficewa daga ƙungiyar Atletico Madrid, lamarin da ke ƙara wa raɗe-raɗin babbar hada-hadar sauya sheƙa akan ɗan wasan. Alvarez ya furta haka ne a wata hira da ESPN bayan wasan da Argentina ta doke Austria da ci 2 da nema a gasar Kofin Duniya da ke cigaba da gudana. A cewarsa, tuni ya fara tattaunawa da jami'an Atletico kuma yana ganin sauya sheƙa a yanzu shi ne abin da ya fi dacewa a gare shi da ƙungiyar. Haka kuma, ɗan wasan…
Read More