Babaji

4783 Posts

Ina son barin Atletico Madrid, inji Alvarez

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ɗan wasan gaba na ƙasar Argentina, Julian Alvarez ya tabbatar da aniyarsa ta ficewa daga ƙungiyar Atletico Madrid, lamarin da ke ƙara wa raɗe-raɗin babbar hada-hadar sauya sheƙa akan ɗan wasan. Alvarez ya furta haka ne a wata hira da ESPN bayan wasan da Argentina ta doke Austria da ci 2 da nema a gasar Kofin Duniya da ke cigaba da gudana. A cewarsa, tuni ya fara tattaunawa da jami'an Atletico kuma yana ganin sauya sheƙa a yanzu shi ne abin da ya fi dacewa a gare shi da ƙungiyar. Haka kuma, ɗan wasan…
Read More

Ƙungiyar IHRC-RFT ta buƙaci a yi adalci kan kisan Malama Ummulkhairi a Kaduna

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kungiyar kare Haƙƙin Ɗan-adam ta Ƙasa da Ƙasa, International Human Rights Commission – Relief Fund Trust (IHRC-RFT) a Nijeriya, ta nuna matukar alhini, damuwa da Allah-wadai kan mummunan kisan gillar da aka yi wa Malama Ummulkhairi a Mararaban Jos, Karamar Hukumar Igabi, Jihar Kaduna, bayan wasu mutane sun zarge ta da wani laifi ba tare da gabatar da ita gaban hukuma ko kotu ba. A wata sanar da Daraktanta na Nijeriya, Amb. Abdullahi Bakoji Adamu ya fitar a ranar Laraba, IHRC-RFT ta ce wannan lamari abin takaici ne matuka kuma ya saba wa dukkan…
Read More

An rantsar da sababbin sanatocin da aka zaɓa a zaɓukan cike gurbi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A yau Laraba Majalisar Dattawa ta rantsar da sababbin sanatoci guda huɗu da suka yi nasara a zaɓukan cike gurbi da Hukumar Zaɓe(INEC) ta gudanar a ranar Asabar da ta gabata. An gudanar da rantsarwar ne ƙarƙashin jagorancin Shugaban majalisar Godswill Akpabio a zaman majalisar a Abuja, inda sabbin sanatocin suka fara wakiltar mazaɓunsu a hukumance bayan karbar takardun shaidar cin zabe daga INEC. Sabbin sanatocin sune Dayo Faduyile mai wakiltar Ondo ta Kudu, Envulu Anza mai wakiltar Nasarawa ta Arewa, Ikeje Asogwu mai wakiltar Enugu ta Arewa, da kuma Olaka Nwogu, Ribas ta…
Read More

Gwamnatin Katsina ta musanta zargin ɗaukar nauyin ‘yan bindiga zuwa aikin Hajji

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a katsina Gwamnatin Jihar Katsina ta musanta da bubbar murya zargin da wani Bashir Kurfi ya yi a wata kafar yaɗa labarai cewa ta dauki nauyin shugabannin 'yan bindiga zuwa aikin Hajjin da ya gabata. A wata takarar sanarwa ɗauke da sa hannun kwamishinan harkokin cinkin gida da tsaro, Dr Nasiru Mu'azu Danmusa ya sanya wa hannu, gwamnatin katsina ta bayana zargin da kurfi yayi a matsayin karya da sharri da kokarin yaudarar alummar jihar katsina da Kuma yunkurin kawo cikas a kokarin da gwamnati da jami'an tsaro ke Yi na kawo zaman lafiya a jihar. Dr…
Read More

Majalisar Dattawa ta amince da ƙudirin dokar kafa ‘yan sandan jihohi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A ranar Laraba Majalisar Dattawa ta kammala aiki akan ƙudirin dokar kafa 'yan sandan jihohi bayan masa karatu na uku, lamarin da ya kawo ƙarshen muhawarar da aka ɗibi tsawon shekaru ana gudanarwa akan tsarin 'yan sanda domin warware matsalolin taɓarɓarewar tsaro a Nijeriya. An cimma nasarar haka ne bayan dogon nazari da kuma da kuma amincewar tabbatar da ƙudirin a dokance daga biyu bisa uku na majalisar. Haka kuma, an amince da kudirin ne a zaman majalisar ne bayan sanatoci sun yi nazari tare da amincewa da sashe-sashe 26 na kudirin a yayin…
Read More

Hukumar SEC ta dakatar da shirin IPO na Matatar Ɗangote, ta gargaɗi ‘yan kasuwa

Hukumar Kula da Kasuwannin Hannayen Jari ta Ƙasa SEC, ta bayar da umarnin dakatar da duk wani tallace-tallace ko kamfen da ke da alaƙa da sayar da hannayen jari na Matatar Ɗangote. Wannan mataki ya biyo bayan gano wasu tallace-tallace da ke yawo a kafafen sada zumunta da sauran hanyoyin sanya hannun jari, duk da cewa babu wata takardar neman amincewa da aka gabatar ko aka amince da ita daga hukumar. Hukumar ta bayyana cewa wasu kamfanonin dillancin hannayen jari da masu tallata saka hannun jari sun fara jawo hankalin mutane su yi rajista ko kuma su tanadi kuɗaɗe domin…
Read More

NAHCON ta fara shirin Hajjin 2027 bayan kammala jigilar alhazan 2026

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Jigilar Alhazan Nijeriya NAHCON, ta kammala jigilar dawowar alhazan ƙasar zuwa gida daga Saudiyya, inda jirgin ƙarshe na alhazan Jihar Zamfara da ya isa a ranar 23 ga Yuni, 2026. Kammala dawowar alhazan ya nuna rufe harkokin hajjin 2026, wanda ya nuna an samu nasarar dawo da alhazan gida lafiya da ƙasa mai tsarki. A wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba, NAHCON ta ce akwai alhazai guda 12 da ke karɓar magani a asibitocin Saudiyya bisa wasu cututtuka mabanbanta da ke damun su. Ta ce tana sanya ido akan halin da…
Read More

Sufeto Janar Disu ya haramta wa ‘yan sanda amfani da Soshiyal Mediya ba da izini ba

Sufeto Janar na ’Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu, ya umarci dukkan jami’ai da ma’aikatan Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya da su daina gudanar da duk wani aiki a kafafen sada zumunta ba tare da izini ba, yana mai gargadin cewa irin waɗannan ayyuka na iya kawo cikas ga mutunci, ƙwarewa da kuma martabar rundunar. A cewar umarnin, an hana jami’an ’yan sanda wallafawa ko rarraba bidiyo, hotuna ko wasu bayanai ba tare da amincewar hukuma ba yayin da suke sanye da kayan aiki na ’yan sanda. Haka kuma, an haramta musu yin tsokaci a bainar jama’a kan harkokin rundunar, fitar da…
Read More

Ƙaddara: Kamfanin Abnur ya nesanta kansa da kalaman jaruma Nafisa Abdullahi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kamfanin Shirya Finafinai na Abnur Entertainment ya nesanta kansa da kalaman jaruma Nafisa Abdullahi ta cikin fim ɗin Ƙaddara, waɗanda suka tayar da ƙura a kafafen sada zumunta a kwanan nan. A wata sanarwa da Abnur ya fitar a ranar Talata, 23 ga Yuni, 2026, ya ce "Ƙaddara" da ɗaukacin waɗanda suka shirya ba su da wata alaƙa da kalaman jarumar da suka shafi batun aure. A cewarsa, Nafisa Abdullahi ra'ayin ƙashin kanta ta bayyana don haka ba ya wakiltar fim ɗin ko sauran waɗanda aka yi shi da su ko wani ɓangarensa. Ya…
Read More

ACF ta kafa kwamitin samar da kuɗaɗe don ciyar da ilimi da tattali gaba a Arewa

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙungiyar Mashawartan Arewa (ACF) ta ƙaddamar da Kwamitin Samar da Kuɗaɗe da nufin tabbatar da tsare gaskiya da adalci wajen ciyar da harkokin ilimi da tattalin arziƙin al'umma gaba a sassan arewacin Nijeriya. A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ranar Talata, ta ce tsohon Sufeto Janar na Rundunar 'Yan sanda, Muhammad Dikko Abubakar ne zai jagoranci kwamitin, inda aka ɗora masa nauyin sanya dabarun jagoranci da tabbatar da nasarar aiwatar da manufofin kuɗaɗen. Da yake jawabi yayin ƙaddamar da kwamitin, Shugaban ACF kuma Wazirin Dutse, Alhaji Bashir Ɗalhatu ya bayyana godiyarsa ga…
Read More