Babaji

4784 Posts

ACF ta kafa kwamitin samar da kuɗaɗe don ciyar da ilimi da tattali gaba a Arewa

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙungiyar Mashawartan Arewa (ACF) ta ƙaddamar da Kwamitin Samar da Kuɗaɗe da nufin tabbatar da tsare gaskiya da adalci wajen ciyar da harkokin ilimi da tattalin arziƙin al'umma gaba a sassan arewacin Nijeriya. A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ranar Talata, ta ce tsohon Sufeto Janar na Rundunar 'Yan sanda, Muhammad Dikko Abubakar ne zai jagoranci kwamitin, inda aka ɗora masa nauyin sanya dabarun jagoranci da tabbatar da nasarar aiwatar da manufofin kuɗaɗen. Da yake jawabi yayin ƙaddamar da kwamitin, Shugaban ACF kuma Wazirin Dutse, Alhaji Bashir Ɗalhatu ya bayyana godiyarsa ga…
Read More

DSS ta kammala hujjojinta akan El-Rufa’i yayin da kotu ta yi watsi da buƙatar sassauta sharuɗɗan beli

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Tsaro ta Farin kaya DSS, ta kammala gabatar wa kotu hujjojinta akan shari'ar tsohon gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufa'i, na tuhumar sa da laifin naɗar hirar Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara akan Harkar Tsaro, Nuhu Ribaɗu ba bisa doka ba. Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi watsi da ƙorafin neman sassauta sharuɗɗan bayar da belin El-Rufa'in daga ɓangaren masu kare shi. A cewar Mai Shari’ar, sharuɗɗan belim masu tsauri da aka kafa tun farko za su cigaba da…
Read More

Sojoji sun kama ɗan ta’adda, sun ƙwato makamai a samamen Kano

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Dakarun Sojojin Nijeriya na Birget ta 3, sun yi nasarar kama wanda ake zargi da ta'addanci da ƙwato makamai da wasu ababe a yayin wani samame a Ƙaramar Hukumar Ɗambatta da ke Jihar Kano. Majiyoyin tsaro sun ce an gudanar da atisayen ne da misalin ƙarfe 10:30 na dare a ranar 21 ga Yuni, 2026 bayan dakarun tsaron sun samu wani bayanin sirri akan wata maɓoyar ɓata-gari da ke ƙauyen Kwanan Dumawa. A yayin atisayen ne aka yi nasarar kama mutum guda da kuma ƙwato ababe da dama daga wajen. Cikin ababen akwai wata…
Read More

Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa ƙudirin kafa dokar ‘yan sandan jihohi

A yau Talata Shugaba Bola Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa ƙudirin gyaran kundin tsarin mulki domin bayar da damar sanya dokar kafa rundunar 'yan sandan jihohi a faɗin Nijeriya. Ƙudirin na neman yin gyare-gyare ne ga wasu sassan kundin tsarin mulkin shekarar 1999 domin samar da sahihin tsarin doka da zai bai wa jihohi damar kafa rundunonin ’yan sandansu. Matakin ya biyo bayan kiraye-kirayen da shugaban ƙasar ya dinga yi na a yi wa kundin tsarin mulki kwaskwarima domin bai wa jihohi damar taka rawar gani wajen samar da tsaro a yankunansu. A watan Fabrairun wannan shekara, Tinubu ya…
Read More

Iyalan malamar Islamiyar da aka halaka a Kaduna sun bayyana yadda suka yi bankwana da ita

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Iyalan Malama Ummulkhairi, wadda malamar Islamiya ce da aka halaka tare da ƙone gawarta bisa zargin ƙarya da aka ɗora mata da ya danganci satar yara a yankin Maraban Jos da ke Ƙaramar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna sun faɗi yadda ganawarsu ta ƙarshe ta kasance. Wasu mazauna yankin ne suka zargi Ummulkhairi, wadda mahaifiyar 'ya'ya huɗu ce, da yunƙurin satar yara a lokacin da take kan hanyar zuwa Islamiyar yamma a ranar Lahadi. Zargin ya yaɗu cikin hanzari, wanda a sanadiyyar haka ne mutane da dama suka farmake ta kana 'yan sanda suka…
Read More

Gwamnan Zamfara ya jajirce kan ƙin sulhu da ‘yan bindiga duk da ci gaba da garkuwa da dattawa 50

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja An yi garkuwa da dattawan ƙauyen Magamin Diddi a Ƙaramar Hukumar Maradun a farkon watan Yuni akan abin da majiyoyi suka bayyana a matsayin sa kai domin sulhu da dabar sanannen jagoran 'yan bindiga, Jammo wanda aka ce shi ke da ikon gudanar da yankin dajin Muntsira. Bincike sun nuna cewa dattawan sun shirya ne da nufin zuwa tattaunawar sasanci da jagoran 'yan bindigar da kuma ƙulla yarjejeniyar zaman lafiya da za su ba mazauna yankunan damar gudanar da harkokinsu na noma cikin aminci ba tare da fargabar wani hari ba. Saidai, a madadin…
Read More

Shettima ya halarci bikin cika shekaru 70 na Sarkin Lafia, ya ƙaddamar da sabbin banyoyi

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya halarci bikin cika shekaru 70 da kuma bikin bankwana da aiki na Sarkin Lafia, Mai Martaba Justice Sidi Bage Muhammad (mai ritaya), wanda aka gudanar a birnin Lafia na Jihar Nasarawa. A jawabinsa, Sanata Shettima ya bayyana cewa samun zaman lafiya mai ɗorewa da ci gaban Najeriya na dogara ne da shugabannin da ke fifita adalci, haɗin kai da jin daɗin jama'a fiye da son zuciya da neman iko. Ya yabawa Sarkin Lafia na 16, inda ya bayyana shi a matsayin abin koyi na shugabanci nagari da Najeriya ke buƙata a dukkan yankunanta.…
Read More

Messi ya karya tarihin yawan zura ƙwallo a gasar Kofin Duniya bayan samun na 17

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Zakaran ƙwallon ƙafa na duniya kuma Kyaftin ɗin Argentina, Lionel Messi ya zama ɗan wasa da ya fi zura ƙwallo a raga a gasar Kofin Duniya na FIFA bayan samun damar zura ta 17 da 18 a wasansu da Austria a birnin Dallas. Messi mai shekaru 39 ya zura ƙwallo na farko ne a raga a minti na 38, lamarin da ya ba shi damar kere tsohon wasan Jamus Miroslav Klose. Akan haka ne ya karya tarihin da Klose ya kafa na mafi yawan ƙwallaye a gasar da ƙwallaye 16. Hakan na zuwa ne…
Read More

Fadar Shugaban Ƙasa ta caccaki Obi kan kira ga Tinubu ya yi murabus bayan saukar firaministan Birtaniya

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Fadar Shugaban Ƙasa ta yi martani ga ɗan takarar shugaban ƙasa a jam'iyyar NDC, Peter Obi, akan kiran sa na cewa Bola Ahmed Tinubu ya yi murabus, inda ta yi watsi da kalaman nasa da kuma bayyana hakan a matsayin yunƙurin ɗauke hankalin jama'a daga muhimman batutuwan ƙasa. Kakakin Shugaban ƙasa, Bayo Onanuga a wata sanarwa ranar Litinin, ya ce Nujeriya ba ta tafiyar da tsarin mulkin majalisa irin na Birtaniya, don haka kwatanta murabus ɗin Firaministan Birtaniya da matsayin Shugaba Tinubu kuskure ne. Onanuga ya bayyana cewa, gwamnatin Shugaba Tinubu ta samu cigaba…
Read More

Katsina: Raɗɗa ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a katsina Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, ya ƙaddamar da shirin rigakafin dabbobi na shekarar 2026 domin daƙile da kuma shawo kan manyan cututtuka masu yaɗuwa da ke addabar shanu, tumaki da awaki a faɗin jihar. An gudanar da bikin kaddamar da shirin ne a kauyen Fulanin Shifdawa da ke Karamar Hukumar Batagarawa, inda aka fara aikin rigakafin a dukkan sassan jihar domin yaki da cututtukan Contagious Bovine Pleuropneumonia (CBPP), Foot and Mouth Disease (FMD) da kuma Peste-des-Petits Ruminants (PPR). A jawabinsa, Gwamna Radda ya bayyana cewa wannan shiri wani muhimmin mataki ne na kare…
Read More